< Anden Kongebog 14 >

1 I Israels Konge Joas's, Joahas's Søns, andet Aar blev Amazia, Joas's, Judas Konges Søn, Konge.
A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Han var fem og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede ni og tyve Aar i Jerusalem; og hans Moders Navn var Joadan fra Jerusalem.
Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
3 Og han gjorde ret for Herrens Øjne, dog ikke som David, hans Fader; han gjorde efter alt det, som Joas, hans Fader, gjorde.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
4 Dog bleve Højene ikke borttagne; Folket ofrede og gjorde Røgelse endnu paa Højene.
Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
5 Og det skete, der Riget blev befæstet i hans Haand, da ihjelslog han sine Tjenere, som havde ihjelslaget Kongen, hans Fader.
Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
6 Men Mordernes Børn dræbte han ikke, som skrevet er i Moses Lovbog, som Herren bød og sagde: Forældre skulle ikke dødes for Børnenes Skyld, og Børnene ikke dødes for Forældrenes Skyld, men hver skal dødes for sin Synds Skyld.
Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
7 Han slog ti Tusinde af Edom i Saltdalen og indtog Sela i samme Krig og kaldte dens Navn Jokthel indtil denne Dag.
Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
8 Da sendte Amazia Bud til Joas, en Søn af Joahas, Jehus Søn, Kongen i Israel, og lod sige: Kom og lader os se hinandens Ansigt!
Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
9 Men Joas, Israels Konge, sendte til Amazia, Judas Konge, og lod sige: Tornebusken, som er paa Libanon, sendte til Cedertræet, som er paa Libanon, og lod sige: Giv min Søn din Datter til Hustru; men vilde Dyr paa Marken, som vare paa Libanon, gik over og nedtraadte Tornebusken.
Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
10 Du har jo slaget Edom, og dit Hjerte gør dig hovmodig; behold din Ære, og bliv i dit Hus; hvi søger du Ulykke, at du skal falde, du og Juda med dig?
Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
11 Men Amazia vilde ikke høre; saa drog Joas, Israels Konge, op, og de saa hinandens Ansigt, han og Amazia, Judas Konge, i Beth-Semes, som hører til Juda.
Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
12 Men Juda blev slagen for Israels Ansigt, og de flyede hver til sit Telt.
Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
13 Og Joas, Israels Konge, fangede Amazia, Judas Konge, en Søn af Joas, Ahasias Søn, i Beth-Semes; og han kom til Jerusalem og nedrev af Jerusalems Mur fra Efraims Port indtil Hjørneporten et Stykke paa fire Hundrede Alen.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
14 Og han tog alt Guldet og Sølvet og alle Karrene, som fandtes i Herrens Hus og i Kongens Hus's Skatkamre, tilmed Børn som Gidsler, og vendte tilbage til Samaria.
Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
15 Men det øvrige af Joas's Handeler, hvad han gjorde og hans Vælde, og hvorledes han stred imod Amazia, Judas Konge, ere de Ting ikke skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Og Joas laa med sine Fædre og blev begraven i Samaria hos Israels Konger, og hans Søn Jeroboam blev Konge i hans Sted.
Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
17 Og Amazia, Joas's Søn, Judas Konge, levede efter Joas's, Joahas's Søns, Israels Konges, Død femten Aar.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
18 Men det øvrige af Amazias Handeler, ere de Ting ikke skrevne i Judas Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
19 Og de indgik et Forbund imod ham i Jerusalem, og han flyede til Lakis; men de sendte efter ham til Lakis og dræbte ham der.
Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
20 Og de førte ham paa Heste, og han blev begraven i Jerusalem hos sine Fædre i Davids Stad.
Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
21 Og alt Judas Folk tog Asaria, men han var seksten Aar gammel, og de gjorde ham til Konge i hans Fader Amazias Sted.
Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
22 Han byggede Elath og bragte den igen til Juda, efter at Kongen laa hos sine Fædre.
Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
23 I Amazias, Joas's Søns, Judas Konges, femtende Aar blev Jeroboam, en Søn af Israels Konge Joas, Konge i Samaria, et og fyrretyve Aar.
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
24 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne; han veg ikke fra nogen af Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
25 Han indtog igen Israels Landemærke fra Hamath af indtil Havet ved den slette Mark efter Herren Israels Guds Ord, som han talte ved sin Tjener Jona, Amithajs Søn, den Profet, som var fra Gath-Hefer.
Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
26 Thi Herren saa Israels Elendighed, som var saare bitter, ja at baade den bundne var intet, og den løsladte var intet, og at der var ingen Hjælper for Israel.
Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
27 Og Herren havde ikke sagt, at han vilde udslette Israels Navn under Himmelen; men han frelste dem ved Jeroboams, Joas's Søns, Haand.
Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
28 Men det øvrige af Jeroboams Handeler og alt det, som han gjorde, og hans Vælde, hvorledes han stred, og at han bragte Damaskus og Hamath, som havde tilhørt Juda, tilbage til Israel, ere de Ting ikke skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
29 Og Jeroboam laa med sine Fædre, med Israels Konger, og hans Søn Sakaria blev Konge i hans Sted.
Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.

< Anden Kongebog 14 >