< 2 Korinterne 3 >
1 Begynde vi atter at anbefale os selv? eller behøve vi, som nogle, Anbefalingsbreve til eder eller fra eder?
Yabon kanmu ne kuma muka fara yi? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi?
2 I ere vort Brev, som er indskrevet i vore Hjerter, og som kendes og læses af alle Mennesker,
Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă santa, yă kuma karanta ta.
3 idet det ligger klart for Dagen, at I ere et Kristi Brev, udfærdiget af os, indskrevet ikke med Blæk, men med den levende Guds Aand, ikke paa Stentavler, men paa Hjerters Kødtavler.
Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.
4 Men en saadan Tillid have vi til Gud ved Kristus,
Amincewa kamar wannan shi ne namu ta wurin Kiristi a gaban Allah.
5 ikke at vi af os selv ere dygtige til at udtænke noget som ud af os selv; men vor Dygtighed er af Gud,
Ba mu da wani abin da za mu nuna cewa da iyawarmu ne muke aikin nan. Iyawarmu daga wurin Allah ne.
6 som ogsaa gjorde os dygtige til at være en ny Pagts Tjenere, ikke Bogstavens, men Aandens; thi Bogstaven ihjelslaar, men Aanden levendegør.
Shi ya sa muka gwaninta a matsayinmu na masu hidimar sabon alkawari ba ta rubutacciyar Dokar ba, amma ta Ruhu; don Dokar, kisa take yi, Ruhu kuwa yana ba da rai.
7 Men naar Dødens Tjeneste, med Bogstaver indristet i Stene, fremtraadte i Herlighed, saa at Israels Børn ikke kunde fæste Øjet paa Mose Ansigt paa Grund af hans Ansigts Herlighed, som dog forsvandt,
To, in hidimar da ta kawo mutuwa, wadda an rubuta a kan allon dutse, ta zo da ɗaukaka har Isra’ilawa suka kāsa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta, ko da yake mai shuɗewa ce,
8 hvorledes skal da ikke Aandens Tjeneste end mere være i Herlighed?
ashe, hidimar Ruhu ba za tă fi wannan ɗaukaka ba?
9 Thi naar Fordømmelsens Tjeneste havde Herlighed, er meget mere Retfærdighedens Tjeneste rig paa Herlighed.
In hidimar da take jawo wa mutane hukunci tana da ɗaukaka haka, to, lalle, hidimar da take kawo adalci za tă fi ta ɗaukaka nesa!
10 Ja, det herlige er jo i dette Tilfælde endog uden Herlighed i Sammenligning med den endnu større Herlighed.
Gama abin da dā take da ɗaukaka, ba ta da ɗaukaka a yanzu, in aka kwatantata da mafificiyar ɗaukaka ta yanzu.
11 Thi naar det, der forsvandt, fremtraadte med Herlighed, da skal meget mere det, der bliver, være i Herlighed.
In kuma aba mai shuɗewa ta zo da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwammame, lalle ne yă kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa!
12 Efterdi vi altsaa have et saadant Haab, gaa vi frem med stor Frimodighed
Da yake muna da bege irin wannan, to, muna da ƙarfin zuciya sosai ke nan.
13 og gøre ikke som Moses, der lagde et Dække over sit Ansigt, for at Israels Børn ikke skulde fæste Øjet paa, at det, der forsvandt, fik Ende.
Mu ba kamar Musa ba ne, wanda ya rufe fuskarsa da lulluɓi, don kada Isra’ilawa su ga ƙarewar ɗaukakan nan mai shuɗewa.
14 Men deres Tanker bleve forhærdede; thi indtil den Dag i Dag forbliver det samme Dække over Oplæsningen af den gamle Pagt uden at tages bort; thi i Kristus er det, at det svinder.
Amma aka sa hankulansu suka dushe, gama har yă zuwa yau akwai lulluɓin nan a duk sa’ad da ake karatun tsohon alkawari. Ba a kawar da shi ba, sai a cikin Kiristi ne kaɗai ake kawar da shi.
15 Men der ligger indtil denne Dag et Dække over deres Hjerte, naar Moses oplæses;
Har yă zuwa yau, duk sa’ad da ake karatun littattafan Musa, lulluɓin nan yakan rufe zukatansu.
16 naar de derimod omvende sig til Herren, da borttages Dækket.
Amma duk sa’ad da wani ya juyo ga Ubangiji, akan kawar da lulluɓin.
17 Men Herren er Aanden, og hvor Herrens Aand er, er der Frihed.
Ubangiji fa, shi ne Ruhu, kuma duk inda Ruhun Ubangiji yake, a nan’yanci yake.
18 Men alle vi, som med ubedækket Ansigt skue Herrens Herlighed som i et Spejl, blive forvandlede til det samme Billede, fra Herlighed til Herlighed, saasom det er fra Aandens Herre.
Mu da ba mu da lulluɓi a fuskokinmu duk muna nuna ɗaukakar Ubangiji, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji wanda yake ruhu kuwa shi ne mai zartar da haka.