< Anden Krønikebog 36 >
1 Og Folket i Landet tog Joakas, Josias's Søn, og de gjorde ham til Konge i hans Faders Sted, i Jerusalem.
Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
2 Joakas var tre og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede tre Maaneder i Jerusalem;
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
3 men Kongen af Ægypten afsatte ham i Jerusalem og straffede Landet paa hundrede Centner Sølv og et Centner Guld.
Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
4 Og Kongen af Ægypten gjorde Eliakim, hans Broder, til Konge over Juda og Jerusalem og omvendte hans Navn til Jojakim; men Neko tog hans Broder Joakas og førte ham til Ægypten.
Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
5 Jojakim var fem og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede elleve Aar i Jerusalem; og han gjorde det, som var ondt for Herrens, hans Guds, Øjne.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
6 Nebukadnezar, Kongen af Babel, drog op imod ham og bandt ham med to Kobberlænker for at føre ham til Babel.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
7 Og Nebukadnezar førte nogle af Herrens Hus's Kar til Babel og lagde dem i sit Tempel i Babel.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
8 Men det øvrige af Jojakims Handeler og hans Vederstyggeligheder, som han gjorde, og det, som fandtes hos ham, se, de Ting ere skrevne i Israels og Judas Kongers Bog; og Jojakin, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Jojakin var otte Aar gammel, der han blev Konge, og regerede tre Maaneder og ti Dage i Jerusalem og gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
10 Men der Aaret var omme, sendte Kong Nebukadnezar hen og lod ham føre til Babel tillige med Herrens Hus's kostelige Kar og gjorde Zedekias, hans Broder, til Konge over Juda og Jerusalem.
Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
11 Zedekias var et og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede elleve Aar i Jerusalem.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
12 Og han gjorde det, som var ondt for Herren, hans Guds, Øjne; han ydmygede sig ikke for Profeten Jeremias, som talte af Herrens Mund.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
13 Tilmed faldt han og af fra Kong Nebukadnezar, som havde ladet ham sværge ved Gud; og han gjorde sin Nakke stiv og forhærdede sit Hjerte og vilde ikke omvende sig til Herren, Israels Gud.
Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
14 Og alle de øverste iblandt Præsterne og Folket forsyndede sig saare meget, idet de efterlignede alle Hedningernes Vederstyggeligheder og besmittede Herrens Hus, som han havde helliget i Jerusalem.
Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
15 Og Herren, deres Fædres Gud, sendte til dem ved sine Sendebud tidligt og ideligt; thi han vilde skaane sit Folk og sin Bolig.
Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
16 Men de bespottede Guds Sendebud og foragtede hans Ord og forhaanede hans Profeter, indtil Herrens Vrede tog til over hans Folk, indtil der var ingen Lægedom mere.
Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
17 Og han førte Kaldæernes Konge op imod dem, og denne ihjelslog deres unge Karle med Sværd udi deres Helligdoms Hus og sparede hverken unge Karle eller Jomfruer, gamle eller udlevede; han gav dem alle i hans Haand.
Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
18 Og alle Kar fra Guds Hus, store og smaa, og Herrens Hus's Skatte og Kongens og hans Fyrsters Skatte førte han alt sammen til Babel.
Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
19 Og de opbrændte Guds Hus og nedbrøde Jerusalems Mure, og de opbrændte alle dens Paladser med Ild, og alle dens kostelige Kar bleve ødelagte.
Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
20 Og han bortførte til Babel dem, som vare overblevne fra Sværdet, og de bleve hans og hans Sønners Tjenere, indtil Persiens Rige fik Magten;
Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
21 at Herrens Ord skulde opfyldes, som var talt ved Jeremias's Mund, indtil Landet havde faaet nok af sine Sabbater; det hvilede den ganske Tid, som Ødelæggelsen varede, indtil halvfjerdsindstyve Aar bleve fyldte.
Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
22 Men i Kyrus's, Kongen af Persiens, første Aar, da Herrens Ord, som var talt ved Jeremias's Mund, var fuldkommet, opvakte Herren Kyrus's, Kongen af Persiens, Aand, at han lod udraabe over sit ganske Rige, ja kundgøre ved Skrift, og sige:
Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
23 Saa siger Kyrus, Kongen i Persien: Herren, Himmelens Gud, har givet mig alle Riger paa Jorden, og han har befalet mig at bygge sig et Hus i Jerusalem, som er i Juda. Hvo der maatte være iblandt eder af alle hans Folk, med ham være Herren hans Gud, og han drage op!
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”