< Anden Krønikebog 33 >

1 Manasse var tolv Aar gammel, der han blev Konge, og regerede fem og halvtredsindstyve Aar i Jerusalem.
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, efter de Hedningers Vederstyggeligheder, som Herren havde fordrevet for Israels Børns Ansigt.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Thi han opbyggede igen de Høje, som Ezekias, hans Fader, havde nedbrudt, og oprejste Altre til Baalerne og gjorde Astartebilleder og tilbad al Himmelens Hær og tjente dem.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 Og han byggede Altre i Herrens Hus, om hvilke Herren havde sagt: I Jerusalem skal mit Navn være evindelig.
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 Tilmed byggede han Altre til hele Himmelens Hær i begge Forgaardene til Herrens Hus.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 Og han lod sine Sønner gaa igennem Ilden i Hinnoms Søns Dal og var en Dagvælger og agtede paa Fugleskrig og brugte Trolddom og beskikkede Spaamænd og Tegnsudlæggere, han gjorde meget ondt for Herrens Øjne til at opirre ham.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Han satte og et udskaaret Billede, som han lod gøre, i Guds Hus, om hvilket Gud havde sagt til David og til Salomo, hans Søn: I dette Hus og i Jerusalem, som jeg har udvalgt fremfor alle Israels Stammer, vil jeg sætte mit Navn evindelig.
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Og jeg vil ikke mere lade Israels Fod fortrænges fra Landet, som jeg bestemte for deres Fædre; kun saafremt de tage Vare paa at gøre alt det, jeg har budet dem, efter hele Loven og Skikkene og Budene ved Mose.
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 Men Manasse forførte Juda og Indbyggerne i Jerusalem til at handle værre end Hedningerne, som Herren havde ødelagt for Israels Børns Ansigt.
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Og Herren talte til Manasse og til hans Folk; men de gave ikke Agt derpaa.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 Derfor lod Herren Kongen af Assyriens Hærførere komme over dem, og de grebe Manasse iblandt Tornebuskene, og de bandt ham med to Kobberlænker og førte ham til Babel.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 Og der han kom i Angest, bad han ydmygelig for Herren sin Guds Ansigt og ydmygede sig saare for sine Fædres Guds Ansigt.
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 Ja, han bad til ham, og Gud bønhørte ham og hørte hans ydmyge Begæring og førte ham tilbage til Jerusalem, til hans Rige; da kendte Manasse, at Herren var Gud.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 Og derefter byggede han den yderste Mur for Davids Stad, Vesten for Gihon i Dalen, og hen til Fiskeporten, og han førte den omkring Ofel og gjorde den saare høj; og han lagde Stridshøvedsmænd i alle Judas faste Stæder.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 Og han borttog de fremmede Guder og hint Billede fra Herrens Hus og alle Altrene, som han havde bygget paa Herrens Hus's Bjerg og i Jerusalem, og han kastede dem uden for Staden.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 Og han istandsatte Herrens Alter og ofrede derpaa Takofre og Lovofre; og han sagde til Juda, at de skulde tjene Herren, Israels Gud.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 Dog ofrede Folket endnu paa Højene, men kun til Herren deres Gud.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 Men det øvrige af Manasses Handeler og hans Bøn til hans Gud og de Seeres Taler, som talte til ham i Herren Israels Guds Navn, se, dette er skrevet i Israels Kongers Krønike.
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 Og hans Bøn, og at han blev bønhørt, og al hans Synd og Forgribelse og de Steder, paa hvilke han byggede Højene og satte Astartebilleder og udskaarne Billeder, førend han blev ydmyget; se, dette er skrevet i Seernes Krønike.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Og Manasse laa med sine Fædre, og de begrove ham i hans Hus, og hans Søn Amon blev Konge i hans Sted.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amon var to og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede to Aar i Jerusalem.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, ligesom Manasse, hans Fader, havde gjort, og til alle de udskaarne Billeder, som Manasse, hans Fader, havde gjort, ofrede Amon og tjente dem.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 Men han ydmygede sig ikke for Herrens Ansigt, som hans Fader Manasse havde ydmyget sig; thi denne Amon gjorde Skylden mangfoldig.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 Og hans Tjenere gjorde et Forbund imod ham og dræbte ham i hans Hus.
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 Men Folket i Landet slog alle dem ihjel, som havde gjort Forbund imod Kong Amon, og Folket i Landet gjorde Josias, hans Søn, til Konge i hans Sted.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.

< Anden Krønikebog 33 >