< Anden Krønikebog 12 >
1 Og det skete, der Roboams Rige var befæstet, og der han var bleven mægtig, da forlod han og hele Israel med ham Herrens Lov.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 Og det skete i Kong Roboams femte Aar, da drog Sisak, Kongen af Ægypten, op imod Jerusalem (thi de havde forsyndet sig imod Herren)
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 med tusinde og to Hundrede Vogne og med tresindstyve Tusinde Ryttere, og der var ikke Tal paa det Folk, som kom med ham af Ægypten: Libyer, Sukiter og Morianer.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 Og han indtog de faste Stæder, som hørte til Juda, og kom til Jerusalem.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Da kom Semaja, Profeten, til Roboam og til de Øverste i Juda, som havde samlet sig til Jerusalem for Sisaks Skyld, og sagde til dem: Saa sagde Herren: I have forladt mig, og jeg har derfor overladt eder i Sisaks Haand.
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Da ydmygede de Øverste udi Israel sig tillige med Kongen, og de sagde: Herren er retfærdig.
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 Og der Herren saa, at de ydmygede sig, da skete Herrens Ord til Semaja og sagde: De have ydmyget sig, jeg vil ikke ødelægge dem; men om en kort Tid vil jeg lade dem undkomme, og min Fortørnelse skal ikke udøses over Jerusalem ved Sisak.
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 Dog skulle de vorde hans Tjenere, at de kunne fornemme, hvad det er at tjene mig og at tjene Landenes Riger.
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 Saa drog Sisak, Kongen af Ægypten, op imod Jerusalem, og han tog Liggendefæet i Herrens Hus og Liggendefæet i Kongens Hus, han tog alting bort; og han tog de Skjolde af Guld, som Salomo havde ladet gøre.
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 Og Kong Roboam lod gøre Kobberskjolde i deres Sted og betroede dem i de øverste Drabanters Haand, som toge Vare paa Døren for Kongens Hus.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 Og det skete, saa tidt Kongen gik ind i Herrens Hus, da kom Drabanterne og bare dem ud, og de bare dem tilbage i Drabanternes Kammer.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Og da han ydmygede sig, blev Herrens Vrede vendt af fra ham, thi han vilde ikke ødelægge ham aldeles; thi der var ogsaa nogle gode Ting i Juda.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 Og Kong Roboam befæstede sig i Jerusalem og regerede; thi Roboam var et og fyrretyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede sytten Aar i Jerusalem, i den Stad, som Herren af alle Israels Stammer havde udvalgt for der at sætte sit Navn; og hans Moders Navn var Naema, den ammonitiske.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Og han gjorde det, som var ondt; thi han beredte ikke sit Hjerte til at søge Herren.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 Men Roboams Handeler, de første og de sidste, ere de ikke skrevne i Profeten Semajas Krønikers Bog og hos Seeren Iddo, hvor han opregner Slægtregistrene? og der var Krige imellem Roboam og Jeroboam alle Dage.
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 Og Roboam laa med sine Fædre, og blev begraven i Davids Stad; og Abia, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.