< 1 Samuel 7 >
1 Og Mændene af Kirjath-Jearim kom og hentede Herrens Ark op og førte den til Abinadabs Hus paa Højen; og de helligede hans Søn Eleasar til at tage Vare paa Herrens Ark.
Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
2 Og fra den Dag, at Arken blev i Kirjath-Jearim, forløb lang Tid, saa at det blev tyve Aar, og hele Israels Hus sukkede efter Herren.
Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
3 Da talede Samuel til al Israels Hus, sigende: Dersom I omvende eder til Herren af eders ganske Hjerte, saa borttager de fremmede Guder og Astartebillederne af eders Midte, og bereder eders Hjerte til Herren og tjener ham alene, og han skal fri eder af Filisternes Haand.
Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
4 Da borttoge Israels Børn Baal og Astartebillederne, og de tjente Herren alene.
Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
5 Og Samuel sagde: Samler al Israel til Mizpa, og jeg vil ydmygeligen bede for eder til Herren.
Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
6 Og de samledes til Mizpa, og de droge Vand op og udøste det for Herrens Ansigt og fastede paa samme Dag og sagde der: Vi have syndet for Herren; og Samuel dømte Israels Børn i Mizpa.
Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
7 Der Filisterne hørte, at Israels Børn havde samlet sig i Mizpa, da droge Filisternes Fyrster op mod Israel; der Israels Børn hørte det, da frygtede de for Filisternes Ansigt.
Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
8 Og Israels Børn sagde til Samuel: Hør ikke op med at raabe for os til Herren vor Gud, at han frelser os fra Filisternes Haand.
Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
9 Saa tog Samuel et diende Lam og ofrede det til et Brændoffer helt for Herren; og Samuel raabte til Herren for Israel, og Herren svarede ham.
Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
10 Og Samuel ofrede Brændofret, og Filisterne kom frem til Krigen imod Israel; men Herren lod tordne med en svar Torden paa den samme Dag over Filisterne og forfærdede dem, og de bleve slagne for Israels Ansigt.
Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
11 Og Israels Mænd droge ud af Mizpa og forfulgte Filisterne; og de sloge dem indtil neden for Beth-Kar.
Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
12 Da tog Samuel en Sten og satte den imellem Mizpa og imellem Sen og kaldte dens Navn Eben-Ezer; og han sagde: Hidindtil har Herren hjulpet os.
Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
13 Saa bleve Filisterne ydmygede og kom ikke ydermere i Israels Landemærke, og Herrens Haand var imod Filisterne, saa længe Samuel levede.
Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
14 Og de Stæder, som Filisterne havde taget fra Israel, kom til Israel igen, fra Ekron og indtil Gath; tilmed udfriede Israel deres Landemærke af Filisternes Haand; men der var Fred imellem Israel og imellem Amoriterne.
Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
15 Og Samuel dømte Israel alle sine Livsdage.
Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
16 Og han gik hvert Aar og vandrede omkring til Bethel og Gilgal og Mizpa og dømte Israel i alle disse Stæder.
Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
17 Og han kom tilbage til Rama, thi der var hans Hus, og der dømte han Israel; og han byggede der Herren et Alter.
Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.