< 1 Samuel 4 >
1 Og Samuels Ord skete til al Israel, og Israel drog ud imod Filisterne til Krig, og de lejrede sig ved Eben-Ezer, men Filisterne havde lejret sig i Afek.
Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
2 Og Filisterne rustede sig imod Israel, og Striden bredte sig ud; og Israel blev slagen for Filisternes Ansigt; og disse sloge i Slagordenen paa Marken ved fire Tusinde Mand.
Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
3 Og der Folket kom til Lejren, da sagde Israels Ældste: Hvorfor har Herren slaget os i Dag for Filisternes Ansigt? lader os hente Herrens Pagts Ark fra Silo og lader den komme midt iblandt os, saa skal den frelse os af vore Fjenders Haand.
Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
4 Og Folket sendte til Silo, og de bare derfra Herren Zebaoths Pagts Ark, han som sidder over Keruber; og de to Elis Sønner, Hofni og Pinehas, vare der med Guds Pagts Ark.
Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
5 Og det skete, der Herrens Pagts Ark kom til Lejren, da skreg al Israel med et stort Frydeskrig, saa at Jorden rystede.
Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
6 Der Filisterne hørte det Frydeskrigs Røst, da sagde de: Hvad er dette for et stort Frydeskrigs Røst i Hebræernes Lejr? Og de fik at vide, at Herrens Ark var kommen til Lejren.
Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
7 Da frygtede Filisterne, thi de sagde: Gud er kommen i Lejren; og de sagde: Ve os! thi der er ikke sket noget som dette tilforn.
sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
8 Ve os! hvo vil fri os af disse herlige Guders Haand? disse ere de Guder, som sloge Ægypten med alle Haande Plager i Ørken.
Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
9 Værer frimodige og værer Mænd, I Filister! at I ikke skulle tjene Hebræerne, som de have tjent eder; ja værer Mænd og strider!
Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
10 Da strede Filisterne, og Israel blev slagen, og de flyede hver til sine Telte, og der skete et saare stort Slag, saa at der faldt af Israel tredive Tusinde Fodfolk.
Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
11 Og Guds Ark blev tagen, og begge Elis Sønner, Hofni og Pinehas, døde.
Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
12 Da løb en Mand af Benjamin fra Slagordenen og kom til Silo paa den samme Dag; og hans Klæder vare sønderrevne, og der var Jord paa hans Hoved.
A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
13 Og han kom, og se, Eli sad paa en Stol ved Siden af Vejen og saa sig om, thi hans Hjerte var saare bange for Guds Ark; der Manden kom til at forkynde det i Staden, da skreg den ganske Stad.
Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
14 Og der Eli hørte Skrigets Røst, da sagde han: Hvad er dette for et Bulders Røst? Og Manden skyndte sig og kom og gav Eli det til Kende.
Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
15 Og Eli var otte og halvfemsindstyve Aar gammel; og hans Øjne vare dunkle, og han kunde ikke se.
wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
16 Og Manden sagde til Eli: Jeg kommer fra Slagordenen, og jeg er flyet fra Slagordenen i Dag; og han sagde: Min Søn, hvad for en Ting skete der?
Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
17 Da svarede den, som bar Budskab, og sagde: Israel flyede for Filisternes Ansigt, og der skete ogsaa et stort Slag paa Folket; og dine to Sønner, Hofni og Pinehas, ere ogsaa døde, og Guds Ark er tagen.
Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
18 Og det skete, der han meldte om Guds Ark, da faldt han baglæns ned af Stolen ved Siden af Porten, og hans Halsben blev brudt, og han døde, thi Manden var gammel og svær; og han havde dømt Israel fyrretyve Aar.
Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
19 Og hans Sønnekone, Pinehas Hustru, var frugtsommelig, nær ved at føde; der hun hørte det Rygte, at Guds Ark var tagen, og at hendes Svoger og hendes Mand var død, da bøjede hun sig ned og fødte, thi hendes Veer betoge hende.
Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
20 Og den Tid hun døde, da sagde de Kvinder, som stode hos hende: Frygt ikke, thi du har født en Søn; men hun svarede ikke og lagde det ikke paa sit Hjerte.
Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
21 Og hun kaldte Barnet Ikabod, sigende: Herligheden er flyttet fra Israel; fordi Guds Ark var tagen, og for hendes Svogers og for hendes Mands Skyld.
Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
22 Og hun sagde: Herligheden er flyttet fra Israel; thi Guds Ark er tagen.
Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”