< 1 Samuel 16 >
1 Og Herren sagde til Samuel: Hvor længe vil du sørge for Saul? og jeg har forkastet ham, at han ikke skal være Konge over Israel; fyld dit Horn med Olie og gak hen, jeg vil sende dig til Bethlehemiteren Isai, thi jeg har udset mig en Konge iblandt hans Sønner.
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
2 Men Samuel sagde: Hvorledes kan jeg gaa? thi Saul skulde høre det og slaa mig ihjel; da sagde Herren: Tag en Kalv af Kvæget med dig, og du skal sige: Jeg er kommen at slagte Slagtoffer for Herren.
Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
3 Og du skal byde Isai til det Slagtoffer; og jeg vil lade dig vide, hvad du skal gøre, og du skal salve mig den, som jeg siger dig.
Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
4 Og Samuel gjorde det, som Herren sagde, og kom til Bethlehem; da forfærdedes de Ældste i Staden og gik ham i Møde og sagde: Er det med Fred, at du kommer?
Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
5 Og han sagde: Det er med Fred, jeg er kommen for at slagte Slagtoffer for Herren, helliger eder og kommer med mig til Slagtofret; og han helligede Isai og hans Sønner og indbød dem til Ofringen.
Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
6 Og det skete, der de kom, da saa han Eliab; og han tænkte: Visseligen er han for Herren hans salvede.
Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
7 Og Herren sagde til Samuel: Se ikke til hans Anseelse eller til hans høje Vækst, thi jeg har forkastet ham; thi jeg agter ikke det, som et Menneske ser paa; thi et Menneske ser det, som er for Øjnene, men Herren ser til Hjertet.
Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
8 Da kaldte Isai ad Abinadab og lod ham gaa forbi for Samuels Ansigt, og han sagde: Denne har Herren ikke heller udvalgt.
Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
9 Derefter lod Isai Samma gaa forbi, og han sagde: Denne har Herren ikke heller udvalgt.
Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
10 Saa lod Isai sine syv Sønner gaa forbi for Samuels Ansigt; men Samuel sagde til Isai: Herren har ikke udvalgt disse.
Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
11 Fremdeles sagde Samuel til Isai: Er det alle Drengene? og han sagde: Den yngste er endnu tilbage, og se, han vogter Smaakvæg; da sagde Samuel til Isai: Send hen og lad ham hente, thi vi sætte os ikke til Bords, før han kommer hid.
Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
12 Da sendte han hen og lod ham føre frem, og han var rødmusset med dejlige Øjne og skøn af Anseelse; da sagde Herren: Staa op, salv ham, thi ham er det.
Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
13 Saa tog Samuel Oliehornet og salvede ham midt iblandt hans Brødre, og Herrens Aand kom heftig over David fra den samme Dag og fremdeles; derefter gjorde Samuel sig rede og gik til Rama.
Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
14 Men Herrens Aand veg fra Saul, og en ond Aand fra Herren forfærdede ham.
To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
15 Da sagde Sauls Tjenere til ham: Se, kære, en ond Aand fra Gud forfærder dig.
Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
16 Vor Herre sige dog til dine Tjenere, som staa for dit Ansigt, at de opsøge en Mand, som forstaar at lege paa Harpe; og det skal ske, naar den onde Aand fra Gud er over dig, og hin leger med sin Haand, da skal det blive godt med dig.
Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
17 Da sagde Saul til sine Tjenere: Kære, ser mig om efter en Mand, som kan lege godt, og fører ham til mig.
Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
18 Da svarede een af de unge Karle og sagde: Se, jeg saa Bethlehemiteren Isais Søn, han forstaar at lege og er vældig til Strid, en Krigsmand og forstandig i Ord, en Mand, som er dejlig af Skikkelse, og Herren er med ham.
Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
19 Da sendte Saul Bud til Isai og lod sige: Send til mig David, din Søn, som er hos Smaakvæget.
Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
20 Da tog Isai et Asen tillige med Brød og en Flaske Vin og et Gedekid og sendte det ved David sin Søns Haand til Saul.
Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
21 Saa kom David til Saul og stod for hans Ansigt; og han elskede ham saare, og han blev hans Vaabendrager.
Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
22 Derefter sendte Saul til Isai og lod sige: Kære, lad David staa for mit Ansigt, thi han har fundet Naade for mine Øjne.
Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
23 Og det skete, naar Aanden fra Gud var over Saul, da tog David Harpen og legede med sin Haand; og Saul blev vederkvæget, og det blev godt med ham, og den onde Aand veg fra ham.
Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.