< 1 Samuel 13 >

1 Saul var. . Aar, da han blev Konge, og han regerede paa andet Aar over Israel.
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 Da udvalgte Saul sig tre Tusinde af Israel, og to Tusinde vare med Saul i Mikmas og paa Bethels Bjerg, og tusinde vare med Jonathan i Benjamins Gibea; men de øvrige Folk lod han fare, hver til sine Telte.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 Og Jonathan slog Filisternes Besætning, som var paa Højen, og Filisterne hørte det; derfor lod Saul blæse i Trompeten i hele Landet og sige: Lad Hebræerne høre det!
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 Og al Israel hørte, at der sagdes: Saul har slaget Filisternes Besætning, og Israel har gjort sig forhadt hos Filisterne; da blev Folket sammenkaldt efter Saul til Gilgal.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 Og Filisterne samledes til at stride med Israel, tredive Tusinde Vogne og seks Tusinde Ryttere og Folk som Sand, der er ved Havbredden i Mangfoldighed; og de droge op og lejrede sig i Mikmas, Østen for Beth-Aven.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 Der Israels Mænd saa sig i Nød (thi Folket blev trængt), da skjulte Folket sig i Hulerne og i Tornebuskene og i Klipperne og i de faste Taarne og i Grøfterne.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 Og Hebræere gik over Jordanen til Gads Land og til Gilead; og Saul var endnu i Gilgal, og alt Folket var forskrækket og fulgte efter ham.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 Og han tøvede i syv Dage til den Tid, som var bestemt af Samuel, men Samuel kom ikke til Gilgal; da adspredtes Folket fra ham.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Da sagde Saul: Fører hid til mig Brændofret og Takofrene; og han ofrede Brændofret.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 Og det skete, der han var færdig med at ofre Brændofret, se, da kom Samuel! og Saul gik ud imod ham at hilse paa ham.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 Da sagde Samuel: Hvad har du gjort? og Saul sagde: Da jeg saa, at Folket adspredtes fra mig, og du kom ikke til den bestemte Tid, og Filisterne vare samlede udi Mikmas,
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 da sagde jeg: Nu komme Filisterne ned mod mig i Gilgal, og jeg har ikke bedet for Herrens Ansigt; da tog jeg Mod til mig og ofrede Brændofret.
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 Da sagde Samuel til Saul: Du har handlet daarligen; du har ikke holdt Herren din Guds Bud, som han bød dig; saa havde Herren nu stadfæstet dit Kongedømme over Israel evindelig.
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 Men nu skal dit Kongedømme ikke bestaa; Herren har opsøgt sig en Mand efter sit Hjerte, og ham har Herren budet at være en Fyrste over sit Folk, fordi du ikke har holdt det, som Herren har befalet dig.
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 Og Samuel gjorde sig rede og gik op fra Gilgal til Gibea i Benjamin; og Saul talte det Folk, som fandtes hos ham, ved seks Hundrede Mand.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 Og Saul og Jonathan, hans Søn, og det Folk, som fandtes hos dem, bleve i Gibea i Benjamin; men Filisterne havde lejret sig i Mikmas.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 Og der uddrog en ødelæggende Skare af Filisternes Lejr i tre Hobe; den ene Hob vendte sig ad Vejen imod Ofra, til Landet Sual;
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 og den anden Hob vendte sig ad Vejen til Beth-Horon; og den tredje Hob vendte sig mod Vejen ved Skellet, der rager frem over Zeboims Dal, ad Ørken til.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Og der blev ingen Smed funden i al Israels Land; thi Filisterne sagde: At Hebræerne ikke skulde gøre Sværd eller Spyd.
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 Derfor maatte al Israel fare ned til Filisterne, at hver kunde faa sit Plovjern og sin Hakke og sin Økse og sin Spade skærpet;
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 og de havde skarpe File til Spader og Hakker og Treforke og Økser, og saa ofte Æggen var sløvet paa Spader, og naar de skulde have en Braad sat ind.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 Og det skete paa Stridens Dag, at der ikke blev funden Sværd eller Spyd i nogen af Folkets Haand, som var med Saul og med Jonathan; dog fandtes der hos Saul og hos Jonathan, hans Søn.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 Og Filisternes Besætning drog ud til Kløftvejen ved Mikmas.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.

< 1 Samuel 13 >