< 1 Samuel 10 >
1 Og Samuel tog en Oliekrukke og øste paa hans Hoved og kyssede ham og sagde: Mon det ikke være saa, at Herren har salvet dig til en Fyrste over hans Arv?
Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
2 Naar du gaar fra mig i Dag, da skal du finde to Mænd ved Rakels Grav i Benjamins Landemærke i Zelza; og de skulle sige til dig: De Aseninder ere fundne, som du gik at lede efter, og se, din Fader har ladet Sagen om Aseninderne fare og er bekymret for eder og siger: Hvad skal jeg gøre for min Søn?
Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
3 Og naar du gaar frem derfra og bedre frem og kommer til Thabors Lund, da skulle tre Mænd finde dig der, som gaa op til Gud i Guds Hus: En, som bærer tre Kid, og en, som bærer tre hele Brød, og en, som bærer en Flaske Vin.
“Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
4 Og de skulle hilse dig og give dig to Brød, og du skal annamme dem af deres Haand.
Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
5 Derefter skal du komme til Guds Høj, hvor Filisternes Besætninger ere; og det skal ske, naar du kommer der til Staden, da skal du møde en Hob Profeter, som komme ned fra Højen, og foran dem skal være Salter og Tromme og Pibe og Harpe, og de skulle profetere.
“Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
6 Og Herrens Aand skal komme heftig over dig, at du skal profetere med dem; og du skal omskiftes til en anden Mand.
Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
7 Og det skal ske, naar disse Tegn indtræffe for dig, saa skal du udføre, hvad du lægger Haand paa; thi Gud er med dig.
Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
8 Og du skal gaa ned for mit Ansigt til Gilgal, og se, jeg vil komme ned til dig til at ofre Brændoffer og at slagte Takofre; syv Dage skal du bie, indtil jeg kommer til dig, saa vil jeg lade dig vide, hvad du skal gøre.
“Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
9 Og det skete, der han vendte Ryggen for at gaa fra Samuel, da gav Gud ham et helt andet Hjerte; og alle disse Ting indtraf samme Dag.
Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
10 Og de kom derhen til Højen, se, da kom en Hob Profeter imod ham, og Guds Aand kom heftig øver ham, og han profeterede midt iblandt dem.
Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
11 Og det skete, der alle de, som kendte ham tilforn, saa det, og se, han profeterede med Profeterne, da sagde Folket, hver til sin Næste: Hvad er det, som er Kis' Søn vederfaret? er og Saul iblandt Profeterne?
Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
12 Da svarede en Mand derfra og sagde: Hvo er dog deres Fader? Derfor blev det til et Ordsprog: Er og Saul iblandt Profeterne?
Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
13 Der han havde holdt op med at profetere, da kom han til Højen.
Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
14 Og Sauls Farbroder sagde til ham og til hans Dreng: Hvor gik I hen? Og han sagde: At lede efter Aseninderne, og der vi saa, at de ikke vare nogensteds, kom vi til Samuel.
Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
15 Da sagde Sauls Farbroder: Kære, kundgør mig, hvad sagde Samuel til eder?
Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
16 Og Saul svarede sin Farbroder: Han gav os til Kende, at Aseninderne vare fundne; men Ordet om Kongedømmet, som Samuel havde sagt, tilkendegav han ham ikke.
Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
17 Og Samuel lod Folket kalde til Hobe til Herren i Mizpa.
Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
18 Og han sagde til Israels Børn: Saa sagde Herren Israels Gud: Jeg førte Israel op af Ægypten, og jeg friede eder af Ægypternes Haand og af alle de Rigers Haand, som fortrykte eder.
ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
19 Men I have i Dag forkastet eders Gud, ham, som frelste eder af alt eders onde og eders Trængsler, og I sagde til ham: Du skal sætte en Konge over os; og nu stiller eder frem for Herrens Ansigt efter eders Stammer og efter eders Tusinder.
Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
20 Og Samuel lod alle Israels Stammer komme frem, da blev Benjamins Stamme ramt.
Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
21 Der han lod Benjamins Stamme komme frem efter dens Slægter, da blev Matris Slægt ramt; og Saul, Kis' Søn blev ramt; og de ledte efter ham, men han fandtes ikke.
Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
22 Da adspurgte de Herren ydermere: Kommer der endnu Nogen herhid? Og Herren sagde: Se, han er skjult ved Tøjet.
Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
23 Da løb de og hentede ham derfra, og han stillede sig midt iblandt Folket; og han var højere end alt Folket fra sin Skulder og derover.
Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
24 Og Samuel sagde til alt Folket: Ser I den, som Herren har udvalgt? thi ingen er som han iblandt alt Folket. Da raabte alt Folket og sagde: Kongen leve!
Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
25 Og Samuel talede til Folket om Kongedømmets Ret og skrev den i en Bog og lod den blive for Herrens Ansigt; saa lod Samuel alt Folket fare, hver til sit Hus.
Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
26 Og Saul gik ogsaa til sit Hus til Gibea; og de af Skaren, hvis Hjerte Gud rørte, gik med ham.
Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
27 Men nogle Belials Børn sagde: Hvad! skal denne frelse os? Og de foragtede ham og bragte ham ikke Skænk; men han var, som han havde været døv.
Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.