< 1 Peter 1 >

1 Peter, Jesu Kristi Apostel, til Udlændingene i Adspredelse i Pontus, Galatien, Kappadokien, Asien og Bithynien,
Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
2 udvalgte efter Gud Faders Forudviden, ved Aandens Helligelse, til Lydighed og Bestænkelse med Jesu Kristi Blod: Naade og Fred vorde eder mangfoldig til Del!
Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
3 Lovet være Gud og vor Herres Jesu Kristi Fader, som efter sin store Barmhjertighed har genfødt os til et levende Haab ved Jesu Kristi Opstandelse fra de døde,
Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
4 til en uforkrænkelig og ubesmittelig og uvisnelig Arv, som er bevaret i Himlene til eder,
Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
5 I, som ved Guds Kraft bevogtes ved Tro til en Frelse, som er rede til at aabenbares i den sidste Tid,
Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
6 i hvilken I skulle fryde eder, om I end nu en liden Stund, hvis saa skal være, bedrøves i mange Haande Prøvelser,
Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
7 for at eders prøvede Tro, som er meget dyrebarere end det forgængelige Guld, der dog prøves ved Ild, maa findes til Ros og Herlighed og Ære i Jesu Kristi Aabenbarelse,
Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
8 ham, som I ikke have set og dog elske, ham, som I, skønt I nu ikke se, men tro, skulle fryde eder over med en uudsigelig og forherliget Glæde,
Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
9 naar I naa Maalet for eders Tro, Sjælenes Frelse.
Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
10 Om denne Frelse have Profeter gransket og ransaget, de, som profeterede om den Naade, der skulde blive eder til Del,
Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
11 idet de granskede over, hvilken eller hvordan en Tid Kristi Aand, som var i dem, henviste til, naar den forud vidnede om Kristi Lidelser og den derpaa følgende Herlighed.
Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
12 Og det blev dem aabenbaret, at det ikke var dem selv, men eder, de tjente med disse Ting, som nu ere blevne eder kundgjorte ved dem, der have forkyndt eder Evangeliet i den Helligaand, som blev sendt fra Himmelen, hvilke Ting Engle begære at skue ind i.
An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
13 Derfor, binder op om eders Sinds Lænder, være ædrue, og sætter fuldt ud eders Haab til den Naade, som bliver eder til Del i Jesu Kristi Aabenbarelse.
Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
14 Som lydige Børn skulle I ikke skikke eder efter de forrige Lyster i eders Vankundighed;
Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
15 men efter den hellige, som kaldte eder, skulle ogsaa I vorde hellige i al eders Vandel;
Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
16 thi der er skrevet: „I skulle være hellige, thi jeg er hellig.”
Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
17 Og dersom I paakalde ham som Fader, der dømmer uden Persons Anseelse efter enhvers Gerning, da bør I vandre i Frygt eders Udlændigheds Tid,
Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
18 vel vidende, at det ikke var med forkrænkelige Ting, Sølv eller Guld, at I bleve løskøbte fra eders tomme Vandel, som var overleveret eder fra Fædrene,
Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
19 men med Kristi dyrebare Blod som et lydeløst og uplettet Lams,
Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
20 han, som var forud kendt før Verdens Grundlæggelse, men blev aabenbaret ved Tidernes Ende for eders Skyld,
An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
21 der ved ham tro paa Gud, som oprejste ham fra de døde og gav ham Herlighed, saa at eders Tro ogsaa er Haab til Gud.
Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
22 Lutrer eders Sjæle i Lydighed imod Sandheden til uskrømtet Broderkærlighed, og elsker hverandre inderligt af Hjertet,
Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
23 genfødte, som I ere, ikke af forkrænkelig, men af uforkrænkelig Sæd, ved Guds levende og blivende Ord. (aiōn g165)
da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn g165)
24 Thi „alt Kød er som Græs, og al dets Herlighed som Græssets Blomst; Græsset visner, og Blomsten falder af;
Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
25 men Herrens Ord bliver evindelig.” Og dette er det Ord, som er forkyndt eder ved Evangeliet. (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn g165)

< 1 Peter 1 >