< Første Kongebog 9 >

1 Og det skete, der Salomo havde fuldendt at bygge Herrens Hus og Kongens Hus og alt, som Salomo begærede, som han havde Lyst til at gøre:
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
2 Da aabenbarede Herren sig for Salomo anden Gang, ligesom han havde aabenbaret sig for ham i Gibeon.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
3 Og Herren sagde til ham: Jeg har hørt din Bøn og din ydmyge Begæring, som du ydmygeligt har bedet med for mit Ansigt, jeg har helliget dette Hus, som du har bygget, at jeg vil sætte mit Navn der indtil evig Tid, og mine Øjne og mit Hjerte skulle være der alle Dage.
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
4 Og du, dersom du vandrer for mit Ansigt, ligesom David, din Fader, vandrede, med et fuldkomment Hjerte og med Oprigtighed til at gøre efter alt det, som jeg har budet dig, og du holder mine Skikke og mine Forskrifter:
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
5 Da vil jeg stadfæste dit Riges Trone over Israel evindeligt, ligesom jeg talte til David, din Fader, og sagde: Dig skal ikke fattes en Mand paa Israels Trone.
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
6 Dersom I vende eder bort, I og eders Børn, fra mig og ikke holde mine Bud og mine Skikke, som jeg gav for eders Ansigt, og I gaa hen og tjene andre Guder og tilbede dem:
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
7 Da vil jeg udrydde Israel fra at være i Landet, som jeg har givet dem, og det Hus, som jeg har helliget til mit Navn, vil jeg forkaste fra mit Ansigt, og Israel skal blive til et Ordsprog og til en Spot iblandt alle Folk.
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
8 Og saa højt end dette Hus monne være, skulle dog alle, som gaa forbi det, grue og hvisle, og de skulle sige: Hvorfor har Herren gjort saaledes ved dette Land og ved dette Hus?
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
9 Og de skulle sige: Fordi de forlode Herren deres Gud, som udførte deres Fædre af Ægyptens Land, og holdt fast ved andre Guder og tilbade dem og tjente dem, derfor har Herren ladet alt dette onde komme over dem.
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
10 Og det skete, der de tyve Aar vare til Ende, i hvilke Salomo byggede de to Huse, Herrens Hus og Kongens Hus,
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
11 og Hiram, Kongen i Tyrus, havde hjulpet Salomo med Cedertræer og Fyrretræer og med Guldet efter al hans Lyst: Da gav Kong Salomo Hiram tyve Stæder i Galilæas Land.
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
12 Og Hiram drog ud af Tyrus for at bese de Stæder, som Salomo havde givet ham, og de behagede ham ikke.
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
13 Og han sagde: Hvad er dette for Stæder, min Broder, som du har givet mig? og han kaldte dem Kabul-Land indtil denne Dag.
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
14 Og Hiram havde sendt til Kongen Hundrede og tyve Centner Guld.
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
15 Saaledes forholdt det sig med de Pligtarbejdere, som Kong Salomo udtog til at bygge Herrens Hus og sit Hus og Millo og Jerusalems Mur og Hazor og Megiddo og Geser: —
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16 Farao, Kongen af Ægypten, var dragen op og havde indtaget Geser og opbrændt den med Ild og ihjelslaget Kananiten, som boede i Staden, og givet sin Datter, Salomos Hustru, den til Medgift.
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
17 Saa byggede Salomo Geser og det nedre Beth-Horon
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18 og Baalath og Thadmor i Ørken udi Landet
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19 og alle de Forraadsstæder, som Salomo havde, og Vognstæder og Stæder til Ryttere og det, som Salomo begærede, som han havde Lyst til at bygge i Jerusalem og paa Libanon og i hele sit Herredømmes Land: —
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
20 Alt det Folk, som var overblevet af Amoriter, Hethiter, Feresiter, Heviter og Jebusiter, de, som ikke vare af Israels Børn,
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
21 deres Børn, som vare overblevne efter dem i Landet, og som Israels Børn ikke havde kunnet ødelægge, dem udtog Salomo til at være arbejdspligtige Tjenere indtil denne Dag.
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
22 Men Salomo gjorde ikke nogen af Israels Børn til Træl; men de vare Krigsmænd og hans Tjenere og hans Fyrster og hans Høvedsmænd og Øverster over hans Vogne og hans Ryttere.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
23 Disse vare de øverste Befalingsmænd, som vare over Salomos Arbejder, fem Hundrede og halvtredsindstyve, de som regerede over det Folk, som gjorde Arbejdet.
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
24 Der Faraos Datter drog op fra Davids Stad ind i sit Hus, som han havde bygget til hende, da byggede han Millo.
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
25 Og Salomo ofrede tre Gange om Aaret Brændofre og Takofre paa det Alter, som han byggede Herren, og gjorde Røgelse paa det, som var for Herrens Ansigt, og han havde fuldendt Huset.
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
26 Og Kong Salomo lod gøre Skibe i Eziongeber, som er ved Eloth, ved det røde Havs Bred, i Edoms Land
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
27 Og Hiram sendte sine Tjenere paa de Skibe, Skibsmænd, forfarne til Søs, med Salomos Tjenere.
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
28 Og de kom til Ofir og hentede derfra fire Hundrede og tyve Centner Guld og førte det til Kong Salomo.
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.

< Første Kongebog 9 >