< Første Kongebog 8 >

1 Da lod Salomo de Ældste af Israel og alle Stammernes Øverster, Fædrenehusenes Fyrster iblandt Israels Børn forsamle sig til Kong Salomo i Jerusalem, for at føre Herrens Pagts Ark op fra Davids Stad, det er Zion.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 Og alle Israels Mænd samledes til Kong Salomo i Ethanim Maaned paa Højtiden, det er den syvende Maaned.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 Og alle de Ældste af Israel kom, og Præsterne opløftede Arken.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 Og de førte Herrens Ark op tillige med Forsamlingens Paulun og alle Helligdommens Redskaber, som vare i Paulunet; Præsterne og Leviterne førte dem op.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Og Kong Salomo og al Israels Menighed, de som vare forsamlede om ham, stode hos ham foran Arken, de ofrede smaat Kvæg og stort Kvæg, som ikke kunde tælles og ikke regnes for Mangfoldigheden.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 Og Præsterne førte Herrens Pagts Ark til dens Sted, til Koret udi Huset, ind i det allerhelligste hen under Kerubernes Vinger.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 Thi Keruberne udbredte Vingerne imod Arkens Sted, og Keruberne dækkede over Arken og oven over dens Stænger.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 Og man drog Stængerne langt ud, og Stængernes Knapper saas fra det hellige lige for Koret, men udenfor kunde de ikke ses, og de bleve der indtil denne Dag.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Der var intet i Arken uden de to Stentavler, som Mose lagde deri ved Horeb, der Herren gjorde Pagt med Israels Børn, der de vare dragne ud fra Ægyptens Land.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Og det skete, der Præsterne gik ud af Helligdommen, da fyldte Skyen Herrens Hus,
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 saa at Præsterne ikke kunde staa at gøre Tjeneste for Skyen; thi Herrens Herlighed fyldte Herrens Hus.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Da sagde Salomo: Herren sagde, at han vilde bo i Mørket.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 Jeg har bygget dig en Boligs Hus, en fast Bolig, at du skal bo deri i al Evighed.
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 Og Kongen vendte sit Ansigt omkring og velsignede al Israels Forsamling, og al Israels Forsamling stod.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 Og han sagde: Lovet være Herren, Israels Gud, som talede med sin Mund til David min Fader og opfyldte det med sin Haand og sagde:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 Fra den Dag, da jeg udførte mit Folk Israel at Ægypten, har jeg ikke udvalgt en Stad af alle Israels Stammer, at man skulde bygge et Hus, for at mit Navn skulde være der; men jeg udvalgte David, at han skulde være over mit Folk Israel.
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 Og det var i min Fader Davids Hjerte, at bygge Herrens, Israels Guds, Navn et Hus.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 Men Herren sagde til David, min Fader: Eftersom det har været i dit Hjerte at bygge mit Navn et Hus, saa gjorde du vel deri, at det var i dit Hjerte.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 Dog skal du ikke bygge det Hus, men din Søn, han som udgaar af dine Lænder, han skal bygge mit Navn et Hus.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 Og Herren har opfyldt sit Ord, som han talede; thi jeg er kommen op i Davids, min Faders, Sted og sidder paa Israels Trone, saaledes som Herren talede, og har bygget Herrens, Israels Guds, Navn et Hus.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 Og jeg har beskikket der et Sted til Arken, hvori Herrens Pagt er, som han gjorde med vore Fædre, der han førte dem ud af Ægyptens Land.
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Og Salomo stod foran Herrens Alter for al Israels Forsamling og udbredte sine Hænder imod Himmelen,
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 og han sagde: Herre, Israels Gud! der er ingen Gud som du i Himmelen oventil eller paa Jorden nedentil, du som holder Pagten og Miskundheden med dine Tjenere, som vandre for dit Ansigt af deres ganske Hjerte;
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 du, som har holdt din Tjener David, min Fader, det, som du har tilsagt ham; du har talt det med din Mund og opfyldt det med din Haand, som det ses paa denne Dag;
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 og nu, Herre Israels Gud! hold din Tjener David, min Fader, det, du har tilsagt ham og sagt: Dig skal ikke fattes en Mand for mit Ansigt, som skal sidde paa Israels Trone, naar ikkun dine Børn bevare deres Vej, at vandre for mit Ansigt, saaledes som du har vandret for mit Ansigt.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 Og nu, Israels Gud! lad dog dit Ord staa fast, som du talede til din Tjener David, min Fader.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 Thi sandelig, monne Gud skulde bo paa Jorden? Se, Himlene og Himlenes Himle kunne ikke rumme dig, langt mindre dette Hus, som jeg har bygget.
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Men vend dit Ansigt til din Tjeners Bøn og til hans ydmyge Begæring, Herre, min Gud! at høre paa det Raab og paa den Bøn, som din Tjener beder for dit Ansigt i Dag:
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 At dine Øjne maa være aabnede over dette Hus Nat og Dag, over dette Sted, om hvilket du har sagt: Mit Navn skal være der, til at høre den Bøn, som din Tjener beder paa dette Sted;
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 og at du vil høre din Tjeners og dit Folk Israels ydmyge Begæring, som de skulle bede paa dette Sted, og at du vil høre paa det Sted, hvor du bor i Himmelen, og vil høre og forlade.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 Naar nogen synder imod sin Næste, og man paalægger ham en Ed, som han skal sværge, og den Ed kommer for dit Alter i dette Hus:
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 Da vil du høre i Himmelen og gøre derefter og dømme dine Tjenere, saa at du fordømmer den ugudelige og fører hans Vej over hans Hoved og retfærdiggør den retfærdige og giver ham efter hans Retfærdighed.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 Naar dit Folk Israel bliver slaget for Fjendens Ansigt, fordi de have syndet imod dig, og de da omvende sig til dig og bekende dit Navn og bede og bønfalde dig om Naade i dette Hus:
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 Da vil du høre i Himmelen og forlade dit Folk Israels Synd og føre dem tilbage i det Land, som du har givet deres Fædre.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 Naar Himmelen bliver tillukt, og der vorder ikke Regn, fordi de have syndet imod dig, og de bede paa dette Sted og bekende dit Navn og omvende sig fra deres Synder, fordi du ydmyger dem:
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 Da vil du høre i Himmelen og forlade dine Tjeneres og dit Folk Israels Synd, fordi du viser dem den gode Vej, paa hvilken de skulle vandre, og vil give Regn over dit Land, som du har givet dit Folk til Arv.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 Naar der vorder Hunger i Landet, naar der vorder Pest, naar der vorder Tørke, Brand i Korn, Græshopper, Kornorme, naar hans Fjende ængster ham i hans Stæders Land, naar der kommer alle Haande Plage, alle Haande Sygdom:
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 Al Bøn, al ydmyg Begæring, som sker af hvert Menneske eller af alt dit Folk Israel, som kender hver sit Hjertes Plage og udbreder sine Hænder til dette Hus,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 den vil du da høre i Himmelen, i den faste Bolig, i hvilken du bor, og forlade og gøre derefter og give enhver efter alle hans Veje, ligesom du kender hans Hjerte; thi du alene kender alle Menneskenes Børns Hjerter;
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 paa det de skulle frygte dig alle de Dage, hvilke de leve i Landet, som du har givet vore Fædre.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 Ja ogsaa den fremmede, som ikke er af dit Folk Israel, naar han kommer fra et langtfra liggende Land for dit Navns Skyld;
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 (thi de skulle høre om dit store Navn og om din stærke Haand og din udrakte Arm) og nogen kommer og beder mod dette Hus:
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 Ham vil du da høre i Himmelen, i den faste Bolig, i hvilken du bor, og gøre efter alt det, som den fremmede raaber til dig om, paa det at alle Folk paa Jorden kunne kende dit Navn og frygte dig, ligesom dit Folk Israel, og at de skulle vide, at dette Hus, som jeg har bygget, er kaldet efter dit Navn.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 Naar dit Folk drager ud i Krigen imod sin Fjende paa den Vej, hvor du sender dem hen, og de bede til Herren, vendte mod den Stad, som du udvalgte, og imod det Hus, som jeg har bygget til dit Navn:
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 Da vil du høre i Himmelen deres Bøn og deres ydmyge Begæring og skaffe dem Ret.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 Naar de synde imod dig, (thi der er intet Menneske, som jo synder) og du bliver vred paa dem og giver dem hen for Fjendens Ansigt, og de, som have fanget dem, føre dem fangne til Fjendens Land, langt borte eller nær hos;
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 og de tage det igen til Hjerte i Landet, hvori de ere fangne, og omvende sig og bede til dig om Naade i deres Land, som have taget dem fangne, og sige: Vi have syndet og handlet ilde, vi have været ugudelige;
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 og de omvende sig til dig af deres ganske Hjerte og af deres ganske Sjæl i deres Fjenders Land, som have taget dem fangne, og de bede til dig, vendte imod deres Land, som du har givet til deres Fædre, imod Staden, som du udvalgte, og Huset, som jeg har bygget for dit Navn:
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 Da vil du høre i Himmelen, i din faste Bolig, i hvilken du bor, deres Bøn og deres ydmyge Begæringer og skaffe dem Ret
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 og forlade dit Folk det, som de have syndet imod dig, og alle deres Overtrædelser, som de have begaaet imod dig, og lade dem finde Barmhjertighed for deres Ansigt, som holde dem fangne, at disse maa forbarme sig over dem;
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 thi de ere dit Folk og din Arv, som du udførte af Ægypten, midt ud af Jernovnen;
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 at dine Øjne maa være aabnede til din Tjeners ydmyge Begæring og til dit Folk Israels ydmyge Begæring, at du vil høre dem i alt det, hvori de paakalde dig.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 Thi du udskilte dig dem af alle Folk paa Jorden til en Arv, saaledes som du talede ved Mose, din Tjener, da du udførte vore Fædre af Ægypten, Herre, Herre!
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 Og det skete, der Salomo havde fuldendt at bede til Herren hele denne Bøn og ydmyge Begæring, da stod han op fra Herrens Alter, fra at knæle paa sine Knæ, med sine Hænder udbredte imod Himmelen,
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 og han stod og velsignede hele Israels Forsamling med høj Røst og sagde:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 Lovet være Herren, som har givet sit Folk Israel Rolighed efter alt det, som han har talt! der blev ikke et Ord til intet af alle hans gode Ord, som han talede ved Mose, sin Tjener.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 Herren vor Gud være med os, ligesom han har været med vore Fædre! Han forlade os ikke og overgive os ikke!
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 at han vil bøje vort Hjerte til sig, saa at vi vandre i alle hans Veje og holde hans Bud og hans Skikke og hans Befalinger, som han har budet vore Fædre,
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 og at disse mine Ord, som jeg har bedet ydmygeligt med for Herrens Ansigt, maa komme nær for Herren vor Gud Dag og Nat, at han vil skaffe sin Tjener Ret og sit Folk, Israel, Ret, hver Dags Sag paa sin Dag,
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 paa det at alle Folk paa Jorden skulle vide, at Herren han er Gud, og ingen ydermere,
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 og at eders Hjerter maa være retskafne for Herren vor Gud til at vandre i hans Skikke og til at holde hans Bud som paa denne Dag.
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Og Kongen og al Israel med ham ofrede Offer for Herrens Ansigt.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 Og Salomo ofrede Takofre, som han ofrede til Herren, to og tyve Tusinde Øksne og Hundrede og tyve Tusinde Faar; saa indviede Kongen og alle Israels Børn Herrens Hus.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 Paa den samme Dag helligede Kongen den mellemste Part af Forgaarden, som var lige for Herrens Hus; thi han lavede der Brændofret og Madofret og Takofrenes Fedtstykker, fordi det Kobberalter, som stod for Herrens Ansigt, var for lidet til at tage imod Brændofret og Madofret og Takofrenes Fedtstykker.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Og Salomo holdt paa den samme Tid Højtiden og al Israel med ham, en stor Forsamling fra Strækningen mellem Hamath og Ægyptens Bæk, for Herrens vor Guds Ansigt i syv Dage og atter i syv Dage, det var fjorten Dage.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 Paa den ottende Dag lod han Folket fare, og de velsignede Kongen, og de gik glade til deres Telte og vel til Mode i Hjertet over alt det gode, som Herren havde gjort David, sin Tjener, og Israel, sit Folk.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.

< Første Kongebog 8 >