< Første Kongebog 4 >

1 Og Kong Salomo var Konge over al Israel.
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
2 Og disse vare de fornemste Befalingsmænd, som han havde: Asarja, Zadoks Søn, var Ypperstepræst;
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
3 Elihoref og Ahia, Sisas Sønner, vare Skrivere; Josafat, Ahiluds Søn, var Historieskriver;
Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
4 og Benaja, Jojadas Søn, var over Hæren; og Zadok og Abjathar vare Præster;
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
5 og Asarja, Nathans Søn, var over Befalingsmændene; og Sabud, Nathans Søn, Præsten, var Kongens Ven;
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
6 og Ahisar var Hovmester; Adoniram, Abdas Søn, var Rentemester.
Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
7 Og Salomo havde tolv Befalingsmænd over al Israel, og de forsynede Kongen og hans Hus; enhver havde en Maaned om Aaret at forsyne ham udi.
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
8 Og disse vare deres Navne: Hurs Søn paa Efraims Bjerg;
Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
9 Dekers Søn i Makaz og i Saalbim og i Beth-Semes og Elon og Beth-Hanan;
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 Heseds Søn i Aruboth, han havde Soko og hele Landet Hefer;
Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 Abinadabs Søn havde hele Egnen Dor, han havde Tafath, Salomos Datter, til Hustru;
Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
12 Baena, Ahiluds Søn, havde Thaanak og Megiddo og hele Beth-Sean, som er ved Zarthan neden for Jisreel fra Beth-Sean indtil Abel-Mehola, indtil paa hin Side Jokmeam;
Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 Gebers Søn var i Ramoth i Gilead; han havde Jairs, Manasse Søns, Byer, som ere i Gilead, han havde Argobs Egn, som er i Basan, tresindstyve store Stæder med Mure og med Kobberstænger;
Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 Ahinadab, Iddos Søn, var i Mahanaim;
Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimaaz var i Nafthali, han tog og Basmath, Salomos Datter, til Hustru;
Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
16 Baena, Husais Søn, var i Aser og i Aloth;
Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 Josafat, Faruas Søn, var i Isaskar;
Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 Simei, Elas Søn, var i Benjamin;
Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 Geber, Uris Søn, var i Gileads Land, i Sihons, den amoritiske Konges, og i Ogs, Kongen af Basans, Land, og det var kun een Befalingsmand, som var i dette Land.
Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
20 Juda og Israel vare mange som Sand, der er ved Havet i Mangfoldighed; de aade og drak og vare glade.
Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
21 Og Salomo var en Herre over alle Rigerne fra Floden til Filisternes Land og indtil Ægyptens Landemærke; de bragte ham Skænk og tjente Salomo alle hans Livsdage.
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 Og den Mad, der gik med for Salomo til hver Dag, var tredive Kor fint Mel og tresindstyve Kor Hvedemel;
Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
23 ti fede Øksne og tyve Græsøksne og hundrede Faar, foruden Hjorte og Raadyr og Bøfler og alle Haande Fjerkræ paa Sti.
shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
24 Thi han herskede i alt det, som laa paa denne Side af Floden, fra Thipsa og indtil Gaza, over alle Konger paa denne Side af Floden; og han havde Fred trindt omkring paa alle sine Sider.
Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
25 Og Juda og Israel boede tryggelig, hver under sit Vintræ og under sit Figentræ, fra Dan og indtil Beersaba, alle Salomos Dage.
A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 Salomo havde og fyrretyve Tusinde Stalde til sine Vognheste og tolv Tusinde Ryttere.
Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 Og disse Befalingsmænd forsynede Kong Salomo og hver den, som nærmede sig til Kong Salomos Bord, hver i sin Maaned; de lode ikke fattes paa noget.
Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
28 Og Byg og Straa til Kørehestene og til Ridehestene førte de hen til det Sted, hvor det skulde være, hver efter Anvisningen.
Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
29 Og Gud gav Salomo Visdom og saare megen Indsigt og en omfattende Forstand, som Sand, der er ved Havets Bred.
Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
30 Og Salomos Visdom var større end alle Østerlændernes Visdom og end alle Ægypternes Visdom.
Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
31 Og han var visere end alle Mennesker, end Esrahiteren Ethan, og Heman og Kalkol og Darda, Mahols Sønner, og hans Navn var berømt hos alle Hedninger trindt omkring.
Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
32 Og han fremsatte tre Tusinde Ordsprog, og hans Sange vare Tusinde og fem.
Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
33 Og han talede om Træerne fra Cederen, som er paa Libanon, og indtil Isopen, som vokser ud af Væggen; og han talede om Dyrene og om Fuglene og om krybende Dyr og om Fiskene.
Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
34 Og man kom fra alle Folk for at høre Salomos Visdom, fra alle Konger paa Jorden, som havde hørt om hans Visdom.
Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.

< Første Kongebog 4 >