< Første Kongebog 3 >
1 Og Salomo besvogrede sig med Farao, Kongen af Ægypten, og tog Faraos Datter og førte hende ind i Davids Stad, indtil han havde fuldendt at bygge sit Hus og Herrens Hus og Jerusalems Mur trindt omkring;
Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
2 ikkun at Folket ofrede paa Højene; thi der var ikke bygget et Hus til Herrens Navn indtil disse Dage.
A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
3 Men Salomo elskede Herren og vandrede efter Davids sin Faders Skikke, kun at han ofrede og gjorde Røgelse paa Højene.
Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
4 Og Kongen gik til Gibeon for at ofre der, thi der var den store Høj, og Salomo ofrede tusinde Brændofre paa dette Alter.
Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
5 Herren aabenbarede sig for Salomo i Gibeon om Natten i en Drøm, og Gud sagde: Begær, hvad jeg skal give dig.
A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
6 Og Salomo sagde: Du har gjort stor Miskundhed imod din Tjener David, min Fader, ligesom han og vandrede for dit Ansigt i Sandhed og i Retfærdighed og i Hjertets Oprigtighed imod dig; og du har bevaret ham denne store Miskundhed og har givet ham en Søn, som sidder paa hans Trone, som det ses paa denne Dag.
Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
7 Og nu, Herre, min Gud! du har gjort din Tjener til Konge i min Fader Davids Sted; men jeg er et ungt Menneske, og jeg forstaar ikke at gaa ud eller ind;
“Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
8 og din Tjener er midt iblandt dit Folk, som du har udvalgt, et stort Folk, saa det ikke kan tælles eller beregnes for Mangfoldigheds Skyld:
Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
9 Saa giv din Tjener et forstandigt Hjerte til at dømme dit Folk og til med Forstand at skelne imellem godt og ondt; thi hvo kan dømme dette dit mægtige Folk?
Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
10 Og det Ord var godt for Herrens Øjne, at Salomo begærede denne Ting.
Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
11 Og Gud sagde til ham: Efterdi du har begæret denne Ting og ikke har begæret dig et langt Liv og ikke har begæret dig Rigdom og ikke har begæret dine Fjenders Sjæl, men har begæret dig Forstand til at holde Dom:
Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
12 Se, saa har jeg gjort efter dit Ord, se, jeg har givet dig et viist og forstandigt Hjerte, at der ikke har været nogen som du før dig; ej heller nogen som du skal opstaa efter dig.
zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
13 Og jeg har endog givet dig det, som du ikke har begæret, baade Rigdom og Ære, saa at der ikke har været nogen som du iblandt Kongerne i alle dine Dage.
Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
14 Og dersom du vandrer i mine Veje, at holde mine Skikke og mine Bud, saaledes som David din Fader har vandret, da vil jeg forlænge dine Dage.
In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
15 Og Salomo vaagnede, og se, det var en Drøm; og han kom til Jerusalem og stod foran Herrens Pagts Ark og ofrede Brændofre og gjorde Takofre og gjorde alle sine Tjenere et Gæstebud.
Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
16 Da kom to Kvinder, som vare Skøger, til Kongen, og de stode for hans Ansigt.
To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
17 Og den ene Kvinde sagde: Hør mig, min Herre! jeg og denne Kvinde boede i eet Hus, og jeg fødte hos hende i Huset.
Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
18 Og det skete paa den tredje Dag, efter at jeg havde født, da fødte ogsaa denne Kvinde; og vi vare sammen, der var ingen fremmed hos os i Huset, uden vi to i Huset.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
19 Og denne Kvindes Søn døde om Natten, thi hun laa paa ham.
“Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
20 Og hun stod op midt om Natten og tog min Søn fra min Side, der din Tjenestekvinde sov, og hun lagde ham i sin Arm, og lagde sin døde Søn i min Arm.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
21 Og jeg stod op om Morgenen, at give min Søn at die, se, da var han død; men om Morgenen gav jeg nøje Agt paa ham, se, da var det ikke min Søn, som jeg havde født.
Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
22 Og den anden Kvinde sagde: Det er ikke saa; thi den levende er min Søn, men den døde er din Søn; og denne sagde: Det er ikke saa; thi den døde er din Søn, men den levende er min Søn; og de talede saa for Kongens Ansigt.
Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
23 Da sagde Kongen: Denne siger: Denne er min Søn, den levende, og den døde er din Søn; og denne siger: Det er ikke saa; thi den døde er din Søn, men den levende er min Søn.
Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
24 Og Kongen sagde: Henter mig et Sværd; og de bragte Sværdet ind for Kongens Ansigt.
Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
25 Da sagde Kongen: Deler det levende Barn i to Dele, og giver den ene Halvdelen og den anden Halvdelen.
Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26 Da sagde Kvinden, hvis Søn den levende var, til Kongen (thi hendes inderste brændte for hendes Søn), ja hun sagde: Hør mig, min Herre! giver hende det levende Barn, og slaar det dog ikke ihjel; men hin sagde: Det skal hverken være mit eller dit, deler det.
Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
27 Og Kongen svarede og sagde: Giver denne det levende Barn, og slaar det ikke ihjel; hun er Moder til det.
Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
28 Og al Israel hørte Dommen, som Kongen havde dømt, og de frygtede for Kongens Ansigt; thi de saa, at Guds Visdom var i ham til at holde Dom.
Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.