< Første Kongebog 20 >

1 Og Benhadad, Kongen i Syrien samlede hele sin Hær, og der var to og tredive Konger med ham og Heste og Vogne; og han drog op og belejrede Samaria og stred imod den.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Og han sendte Bud til Akab, Israels Konge, til Staden.
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 Og han lod ham sige: Saa siger Benhadad: Dit Sølv og dit Guld, det er mit, og dine smukkeste Hustruer og Børn, de ere mine.
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 Og Israels Konge svarede og sagde: Efter dine Ord skal det være, min Herre Konge! jeg er din og alt det, jeg har.
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 Derefter kom Budene igen og sagde: Saa siger Benhadad: Efterdi jeg sendte til dig og lod sige: Du skal give mig dit Sølv og dit Guld og dine Hustruer og dine Børn:
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 Saa vil jeg sende mine Tjenere til dig i Morgen paa denne Tid, og de skulle ransage i dit Hus og i dine Tjeneres Huse, og det skal ske, alt det, som er lysteligt for dine Øjne, skulle de lægge i deres Hænder og tage det bort.
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 Da kaldte Israels Konge ad alle Landets ældste og sagde: Kære, mærker og ser, at denne søger det, som ondt er; thi han sendte til mig om mine Hustruer og om mine Børn og om mit Sølv og om mit Guld, og jeg har ikke nægtet ham det.
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 Da sagde alle de ældste og alt Folket til ham: Du skal ikke adlyde og ikke samtykke.
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 Da sagde han til Benhadads Bud: Siger min Herre Kongen: Alt det, du sendte til din Tjener første Gang om, vil jeg gøre, men denne Gerning kan jeg ikke gøre, og Budene gik og bragte ham Svar igen.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 Da sendte Benhadad til ham og lod sige: Guderne gøre mig nu og fremdeles saa og saa, om Støvet af Samaria skal blive nok til, at alt Folket, som er i Følge med mig, skal kunne føre hver en Haandfuld derfra.
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 Da svarede Israels Konge og sagde: Siger: Den, som ombinder Bæltet, skal ikke rose sig som den, der løser det.
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Og det skete, der han hørte dette Ord, medens han drak, han og Kongerne i Teltene, da sagde han til sine Tjenere: Sætter an; og de satte an imod Staden.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 Og se, en Profet gik frem til Akab, Israels Konge, og sagde: Saa sagde Herren: Har du set hele denne store Hob? se, jeg vil give den i Dag i din Haand, at du skal fornemme, at jeg er Herren.
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Og Akab sagde: Ved hvem? og han sagde: Saa siger Herren: Ved Landshøvdingenes Drenge; og han sagde: Hvem skal begynde Striden? og han sagde: Du.
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 Saa talte han Landshøvdingenes Drenge, og de vare to Hundrede og to og tredive; og efter dem talte han hele Folket, alle Israels Børn, syv Tusinde.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 Og de droge ud om Middagen; og Benhadad drak og var drukken i Teltene, han og Kongerne, nemlig de to og tredive Konger, som hjalp ham.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 Og Landshøvdingenes Drenge droge først ud; og Benhadad sendte nogle hen, og de gave ham til Kende og sagde: Der drager Mænd ud fra Samaria.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 Og han sagde: Dersom de ere uddragne for Freds Skyld, saa griber dem levende, og dersom de ere uddragne for Krigs Skyld, saa griber dem levende!
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 Da de vare uddragne af Staden, nemlig Landshøvdingenes Drenge og Hæren, som fulgte dem:
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 Da sloge de hver sin Mand, og Syrerne flyede, og Israel forfulgte dem; og Benhadad, Kongen af Syrien, undkom paa en Hest med Rytterne.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Og Israels Konge drog ud og slog Heste og Vogne og slog Syrerne med et stort Slag.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 Da gik Profeten frem til Israels Konge og sagde til ham: Gak, forstærk dig, og vid og se, hvad du skal gøre; thi naar Aaret er omme, vil Kongen af Syrien drage op imod dig.
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 Og Kongen af Syriens Tjenere sagde til ham: Deres Guder ere Bjergenes Guder, derfor ere de stærkere end vi; men lader os stride imod dem paa det jævne Land; hvad gælder det, om vi ikke skulle blive stærkere end de?
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 Og gør denne Gerning: Tag Kongerne bort, hver fra sin Plads, og sæt Statholdere i deres Sted!
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Og tæl dig en Hær, som denne Hær var, som er falden for dig, og Heste som de Heste og Vogne som de Vogne, og lader os stride imod dem paa det jævne Land; hvad gælder det, om vi ikke skulle blive stærkere end de? og han adlød deres Røst og gjorde saa.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 Og det skete, der Aaret var omme, da talte Benhadad Syrerne og drog op til Afek, til Krigen imod Israel.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 Og Israels Børn bleve talte og forsynede, og de droge imod dem; og Israels Børn lejrede sig imod dem som to smaa Gedehjorde; men Syrerne havde opfyldt Landet.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 Og der kom en Guds Mand frem og talte til Israels Konge og sagde: Saa sagde Herren: Fordi Syrerne have sagt: Herren er Bjergenes Gud og ikke Dalenes Gud, derfor har jeg givet hele denne store Hob i din Haand, for at I skulle fornemme, at jeg er Herren.
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 Og disse lejrede sig over for dem syv Dage, og det skete paa den syvende Dag, da begyndte Slaget, og Israels Børn sloge Syrerne, hundrede Tusinde Fodfolk paa een Dag.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 Og de, som bleve tilovers, flyede til Afek ind i Staden, og Muren faldt paa syv og tyve Tusinde Mænd, som vare blevne tilovers; og Benhadad flyede og kom i Staden, fra et Kammer til et andet.
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 Da sagde hans Tjenere til ham: Kære, se, vi have hørt, at Israels Konger ere naadige Konger; kære, lader os lægge Sække om vore Lænder og Reb om vore Hoveder og gaa ud til Israels Konge, maaske han lader din Sjæl leve.
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 Og de bandt Sække om deres Lænder og Reb om deres Hoveder, og de kom til Israels Konge og sagde: Benhadad, din Tjener siger: Kære, lad min Sjæl leve; og han sagde: Lever han endnu? han er min Broder.
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Og Mændene udlagde sig det til det gode og skyndte sig med at faa ham til at sige, om det var hans Alvor, og de sagde: Benhadad er din Broder; og han sagde: Gaar ind, henter ham hid; da gik Benhadad ud til ham, og han lod ham stige op paa Vognen.
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Og Benhadad sagde til ham: Jeg vil give dig igen de Stæder, som min Fader tog fra din Fader, og du maa anlægge dig Gader i Damaskus, ligesom min Fader anlagde i Samaria; og jeg, sagde Akab, vil med den Pagt lade dig fare. Saa gjorde han en Pagt med ham og lod ham fare.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Og en Mand af Profeternes Børn sagde til sin Næste ved Herrens Ord: Kære, slaa mig; men Manden vægrede sig ved at slaa ham.
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 Da sagde han til ham: Fordi du ikke adlød Herrens Røst, se, da skal en Løve slaa dig, naar du gaar fra mig; og han gik fra ham, og en Løve traf ham og slog ham.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Og han traf en anden Mand og sagde: Kære, slaa mig; og Manden slog ham haardt og saarede ham.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Da gik Profeten og stod for Kongen paa Vejen og gjorde sig ukendelig med et Klæde over sine Øjne.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 Og det skete, da Kongen drog forbi, at han raabte til Kongen og sagde: Din Tjener var dragen ud midt i Krigen, og se, en Mand veg af Vejen og førte en Mand til mig og sagde: Forvar denne Mand; dersom han savnes, da skal dit Liv være i Stedet for hans Liv, eller du skal betale et Centner Sølv.
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 Og det skete, der din Tjener havde at gøre her og der, da var han ikke mere der; og Israels Konge sagde til ham: Saa er din Dom, du har selv fældet den.
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 Da skyndte han sig og tog Klædet bort fra sine Øjne, og Israels Konge kendte ham, at han var en af Profeterne.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 Og han sagde til ham: Saa sagde Herren: Fordi du slap den Mand, som jeg har sat i Band, af din Haand, da skal din Sjæl være i Stedet for hans Sjæl, og dit Folk i Stedet for hans Folk.
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 Saa drog Israels Konge til sit Hus, ilde tilfreds og vred; og han kom til Samaria.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.

< Første Kongebog 20 >