< Første Kongebog 15 >

1 Og i det attende Kong Jeroboams, Nebats Søns, Aar blev Abiam Konge over Juda.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 Han regerede tre Aar i Jerusalem, og hans Moders Navn var Maeka, Abisaloms Datter.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 Og han vandrede i alle sin Faders Synder, som han gjorde før ham, og hans Hjerte var ikke helt med Herren hans Gud, som Davids, hans Faders, Hjerte.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 Men Herren hans Gud gav ham et Lys i Jerusalem for Davids Skyld, ved at han oprejste hans Søn efter ham og lod Jerusalem bestaa;
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 fordi David gjorde det, som ret var for Herrens Øjne, og veg ikke fra alt det, som han bød ham, alle sine Livs Dage, uden i den Handel med Hethiteren Uria.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 Og der var Krig imellem Roboam og imellem Jeroboam alle hans Livs Dage.
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 Men det øvrige af Abiams Handeler og alt det, som han har gjort, ere de Ting ikke skrevne i Judas Kongers Krønikers Bog? Og der var Krig imellem Abiam og Jeroboam.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 Og Abiam laa med sine Fædre, og de begrove ham i Davids Stad, og Asa, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Og i det tyvende Jeroboams, Israels Konges, Aar blev Asa Konge over Juda.
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 Og han regerede et og fyrretyve Aar i Jerusalem, og hans Moders Navn var Maeka, Abisaloms Datter.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 Og Asa gjorde det, som ret var for Herrens Øjne, som David hans Fader.
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 Og han fordrev Skørlevnerne af Landet og bortskaffede alle stygge Afguder, som hans Fædre havde gjort.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 Tilmed afsatte han Maeka, sin Moder, at hun ikke skulde være Dronning, fordi hun havde gjort sig et grueligt Billede af Astarte, og Asa udryddede hendes gruelige Billede og opbrændte det ved Kedrons Bæk.
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 Men Højene toges ikke bort; dog var Asas Hjerte helt med Herren alle hans Dage.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 Og ban førte de Ting, som hans Fader havde helliget, og hvad som han selv havde helliget, ind i Herrens Hus, Sølv og Guld og Kar.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 Og der var Krig mellem Asa og Baesa, Israels Konge, alle deres Dage.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 Thi Baesa, Israels Konge, drog op imod Juda og byggede Rama, for ikke at tilstede Asa, Judas Konge, at nogen drog ud eller kom ind.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 Da tog Asa alt det Sølv og Guld, de Ting, som vare blevne tilovers af Herrens Hus's Liggendefæ og af Kongens Hus's Liggendefæ, og gav sine Tjenere dem i Hænderne, og Kong Asa sendte dem til Benhadad, en Søn af Tabrimmon, Hesions Søn, Kongen i Syrien, som boede i Damaskus og lod sige:
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 Der er en Pagt imellem mig og imellem dig, imellem min Fader og imellem din Fader, se, jeg sender dig Skænk, Sølv og Guld, drag hen, gør til intet din Pagt med Baesa, Israels Konge, at han maa drage op fra mig.
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 Og Benhadad adlød Kong Asa og sendte de Hærførere, som han havde, imod Israels Stæder og slog Ijon og Dan og Abel-Beth-Maaka og hele Kinneroth, tillige med alt Nafthalis Land.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 Og det skete, der Baesa hørte det, da lod han af fra at bygge Rama og blev i Thirza.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Saa lod Kong Asa hele Juda opbyde, der blev ingen fri, og de toge Stenene bort af Rama tillige med Tømmeret der, som Baesa havde bygget med, og Kong Asa byggede dermed Geba i Benjamin og Mizpa.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 Men det øvrige af alle Asas Han deler og al hans Vælde og alt, hvad han har gjort, og de Stæder, som han har bygget, ere de Ting ikke skrevne i Judas Kongers Krønikers Bog? Dog i sin Alderdoms Tid blev han syg i sine Fødder.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 Og Asa laa med sine Fædre og blev begraven med sine Fædre i Davids, sin Faders Stad, og Josafat, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 Og Nadab, Jeroboams Søn, blev Konge over Israel i det andet Asas, Judas Konges, Aar og regerede over Israel to Aar.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 Og han gjorde det onde for Herrens Øjne og vandrede i sin Faders Veje og i hans Synd, som han kom Israel til at synde med.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 Men Baesa, Ahias Søn, af Isaskars Hus, gjorde et Forbund imod ham, og Baesa slog ham ved Gibbethon, som hørte Filisterne til, der Nadab og al Israel belejrede Gibbethon.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 Og Baesa slog ham ihjel i det tredje Asas, Judas Konges, Aar og blev Konge i hans Sted.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 Og det skete, der han var Konge, da slog han hele Jeroboams Hus, han lod ikke nogen af Jeroboams blive tilovers, som havde Aande, indtil han havde ødelagt ham, efter Herrens Ord, som han talte ved Siloniteren Ahia, sin Tjener,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 for Jeroboams Synders Skyld, som han syndede med, og som han kom Israel til at synde med, og for den Opirrelse, med hvilken han opirrede Herren, Israels Gud.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 Men det øvrige af Nadabs Handeler, og alt det, som han har gjort, ere de Ting ikke skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 Og der var Krig imellem Asa og imellem Baesa, Israels Konge, alle deres Dage.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 I det tredje Asas, Judas Konges, Aar blev Baesa, Ahias Søn, Konge over al Israel i Thirza, fire og tyve Aar.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 Og han gjorde det onde for Her-Tens Øjne og vandrede i Jeroboams Vej og i hans Synd, som han kom Israel til at synde med.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.

< Første Kongebog 15 >