< Første Kongebog 11 >

1 Og Kong Salomo elskede mange fremmede Kvinder foruden Faraos Datter, moabitiske, ammonitiske, edomitiske, zidonitiske, hethitiske,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 af de Hedninger, om hvilke Herren havde sagt til Israels Børn: Gaar ikke ind til dem og lader dem ikke komme ind til eder, de skulle visselig bøje eders Hjerter efter deres Guder; ved disse hængte Salomo med Kærlighed.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Og hans Hustruer vare syv Hundrede Fruer og tre Hundrede Medhustruer; og hans Hustruer bøjede hans Hjerte.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Og det skete, den Tid Salomo blev gammel, bøjede hans Hustruer hans Hjerte efter andre Guder; og hans Hjerte var ikke helt med Herren hans Gud som Davids, hans Faders, Hjerte.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Thi Salomo vandrede efter Astoreth, Zidoniernes Gud, og efter Milkom, Ammoniternes Vederstyggelighed.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 Og Salomo gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, og vandrede ikke fuldkommelig efter Herren som David, hans Fader.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Da byggede Salomo en Høj til Kamos, Moabs Vederstyggelighed, paa Bjerget, som ligger lige for Jerusalem, og til Molek, Ammons Børns Vederstyggelighed.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Og saa gjorde han for alle sine fremmede Kvinder, som gave Røgelse og ofrede til deres Guder.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 Og Herren blev vred paa Salomo, fordi hans Hjerte bøjede sig fra Herren, Israels Gud, som havde aabenbaret sig for ham to Gange,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 og som havde givet ham Befaling om denne Sag, at han ikke skulde vandre efter andre Guder, og han holdt ikke det, som Herren havde befalet.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Derfor sagde Herren til Salomo: Efterdi saadant er hos dig, og du ikke har holdt min Pagt og mine Skikke, som jeg har budet dig, vil jeg visselig rive Riget fra dig og give din Tjener det.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Dog vil jeg ikke gøre det i dine Dage, for Davids, din Faders, Skyld; af din Søns Haand vil jeg rive det.
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Dog vil jeg ikke rive det ganske Rige fra dig; een Stamme vil jeg give din Søn, for Davids, min Tjeners Skyld, og for Jerusalems Skyld, som jeg har udvalgt.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 Og Herren opvakte Salomo en Modstander, nemlig Edomiteren Hadad, han var af Kongens Sæd i Edom.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Thi det skete, der David var i Edom, der Joab, Stridshøvedsmanden, drog op at begrave de ihjelslagne, da slog han alt Mandkøn i Edom.
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 Thi Joab og al Israel bleve der seks Maaneder, indtil han havde udryddet alt Mandkøn i Edom.
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Men Hadad flyede, han og nogle edomitiske Mænd af hans Faders Tjenere med ham, for at komme til Ægypten, og Hadad var en liden Dreng.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Og de droge op fra Midian og kom til Paran, og de toge Mænd med sig fra Paran og kom til Ægypten til Farao, Kongen i Ægypten, og han gav ham et Hus og tilsagde ham Underholdning og gav ham Land.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 Og Hadad fandt stor Naade for Faraos Øjne; og han gav ham til Hustru sin Hustrus Søster, Dronning Takfenes's Søster.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Og Takfenes's Søster fødte ham Genubath, hans Søn, og Takfenes afvante ham udi Faraos Hus, og Genubath var i Faraos Hus midt iblandt Faraos Børn.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Der Hadad hørte i Ægypten, at David laa med sine Fædre, og at Joab, Stridshøvedsmanden, var død, da sagde Hadad til Farao: Lad mig fare, at jeg kan drage til mit Land.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 Og Farao sagde til ham: Men hvad fattes dig hos mig? og se, du søger at drage til dit Land; og han sagde: Mig fattes intet, men lad mig dog fare.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 Gud opvakte ham ogsaa en Modstander, Reson, Eljadas Søn, som flyede fra sin Herre Hadad-Eser, Kongen af Zoba,
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 og samlede Mænd til sig og blev Høvedsmand for en Trop, der David slog dem; og de droge til Damaskus og boede i den og regerede i Damaskus.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Og han var Israels Modstander alle Salomos Dage, og det var foruden det onde, som Hadad gjorde; og han hadede Israel og blev Konge over Syrien.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Og Jeroboam, Nebats Søn, en Efratiter fra Zareda, hvis Moders Navn var Zerua, en Enke, Salomos Tjener, han opløftede ogsaa Haand imod Kongen.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 Og dette er Sagen, hvorfor han opløftede Haand imod Kongen: Salomo byggede Millo og tillukkede det aabne Sted paa Davids sin Faders Stad.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 Og Manden Jeroboam var et dygtigt Menneske, og der Salomo saa den unge Karl, at han udrettede Gerningen vel, da beskikkede han ham over alt Josefs Hus's Arbejde.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 Og det skete paa samme Tid, da Jeroboam gik ud af Jerusalem, at Siloniteren Ahia, Profeten, traf ham paa Vejen og han var iført et nyt Klædebon, og de to vare alene paa Marken.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Og Ahia tog fat i det nye Klædebon, som han havde paa sig, og han rev det i tolv Stykker.
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 Og han sagde til Jeroboam: Tag ti Stykker til dig; thi saa siger Herren, Israels Gud: Se, jeg river Riget af Salomos Haand og vil give dig de ti Stammer.
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 Men han skal have den ene Stamme for min Tjener Davids Skyld og for Jerusalems Stads Skyld, som jeg udvalgte af alle Israels Stammer;
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 fordi de have forladt mig og nedbøjet sig for Astoreth, Zidoniernes Gud, for Kamos, Moabiternes Gud, og for Milkom, Ammons Børns Gud, og de have ikke vandret i mine Veje til at gøre, hvad ret var for mine Øjne, og mine Skikke og mine Forskrifter som David hans Fader.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Dog vil jeg ikke tage noget af Riget ud af hans Haand; men jeg vil lade ham blive en Fyrste i alle hans Livs Dage, for Davids min Tjeners Skyld, som jeg udvalgte, som holdt mine Bud og mine Skikke.
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 Men jeg vil tage Riget ud af hans Søns Haand og give dig de ti Stammer.
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 Og jeg vil give hans Søn en Stamme, paa det David, min Tjener, skal alle Dage have et Lys for mit Ansigt i Jerusalem, den Stad, som jeg udvalgte mig, at sætte mit Navn der.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Og dig vil jeg antage, at du skal regere over alt det, din Sjæl begærer, og du skal være Konge over Israel.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Og det skal ske, dersom du hører alt det, jeg byder dig, og vandrer i mine Veje og gør det, som er ret for mine Øjne, at holde mine Skikke og mine Bud, saaledes som David, min Tjener, gjorde: Da vil jeg være med dig og bygge et bestandigt Hus, saaledes som jeg byggede David, og give dig Israel.
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 Og jeg vil ydmyge Davids Sæd for denne Sags Skyld, dog ikke alle Dage.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Og Salomo søgte efter at dræbe Jeroboam; da gjorde Jeroboam sig rede og flyede til Ægypten, til Sisak, Kongen i Ægypten, og blev i Ægypten, indtil Salomo døde.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Men det øvrige af Salomos Handeler, og alt, hvad han har gjort, og hans Visdom, ere de Ting ikke skrevne i Salomos Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Men Dagene, som Salomo var Konge i Jerusalem over al Israel, vare fyrretyve Aar.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 Og Salomo laa med sine Fædre og blev begraven i Davids, sin Faders, Stad; og Roboam, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< Første Kongebog 11 >