< Første Kongebog 1 >
1 Og Kong David var gammel, kommen til Aars, og de dækkede ham til med Klæder, men han blev ikke varm.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Da sagde hans Tjenere til ham: Lad dem oplede til vor Herre Kongen en ung Pige, en Jomfru, at hun kan staa for Kongens Ansigt og pleje ham og ligge i din Arm, og min Herre Kongen kan blive varm.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 Og de ledte efter en dejlig ung Pige inden alt Israels Landemærke, og de fandt Abisag, den sunamitiske, og de førte hende til Kongen.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Og Pigen var over maade dejlig, og hun plejede Kongen og tjente ham; men Kongen kendte hende ikke.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Og Adonia, Hagiths Søn, op højede sig selv og sagde: Jeg vil være Konge; og han skaffede sig Vogne og Ryttere og halvtredsindstyve Mænd, som løb foran ham
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Og hans Fader havde ikke bedrøvet ham i sine Dage ved at sige: Hvorfor gør du saaledes? og han var saare dejlig af Skikkelse, og hans Moder havde født ham næst efter Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Og han førte Tale med Joab, Zerujas Søn, og med Præsten Abjathar, og de understøttede Adonia.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 Men Zadok, Præsten, og Benaja, Jojadas Søn, og Nathan, Profeten, og Simei og Rei og de vældige, som David havde, de vare ikke med Adonia.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Og Adonia slagtede stort Kvæg og smaat Kvæg og fedt Kvæg ved Soheleths Sten, som ligger ved En-Rogel, og han indbød alle sine Brødre, Kongens Sønner, og alle Judas Mænd, Kongens Tjenere.
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 Men Nathan, Profeten, og Benaja og de vældige og Salomo, sin Broder, indbød han ikke.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Da talede Nathan til Bathseba, Salomos Moder, sigende: Har du ikke hørt, at Adonia, Hagiths Søn, er bleven Konge, og vor Herre David ved det ikke?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Saa gak nu, kære, jeg vil raade dig et Raad, at du skal redde dit Liv og din Søn Salomos Liv.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Gak hen og træd ind til Kong David, og du skal sige til ham: Du, min Herre Konge, har du ikke tilsvoret din Tjenestekvinde og sagt: Din Søn Salomo skal være Konge efter mig, og han skal sidde paa min Trone; hvorfor er da Adonia bleven Konge?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Se, naar du endnu taler der med Kongen, vil og jeg komme efter dig og fuldende din Tale.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 Og Bathseba kom ind til Kongen i Kammeret; og Kongen var saare gammel, og Abisag, den sunamitiske, tjente Kongen.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 Og Bathseba nejede og bøjede sig dybt for Kongen; da sagde Kongen: Hvad fattes dig?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 Og hun sagde til ham: Min Herre! du har tilsvoret din Tjenestekvinde ved Herren din Gud: Din Søn Salomo skal blive Konge efter mig, og han skal sidde paa min Trone.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Men nu, se, Adonia er bleven Konge, og nu, min Herre Konge, du ved det ikke.
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 Og han har slagtet Øksne og fedt Kvæg og Faar i Mangfoldighed, og han har indbudt alle Kongens Sønner og Abjathar, Præsten, og Joab, Stridshøvedsmanden; men han har ikke indbudt din Tjener Salomo.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 Men du, min Herre Konge, al Israels Øjne se paa dig, at du skal give dem til Kende, hvo der skal sidde paa min Herre Kongens Trone efter ham.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Ellers sker det, naar min Herre Kongen ligger med sine Fædre, at jeg og min Søn Salomo maa være som Syndere.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 Og se, da hun endnu talede med Kongen, da kom Profeten Nathan.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 Og de gave Kongen det til Kende og sagde: Se, der er Profeten Nathan; og der han kom for Kongens Ansigt, da bøjede han sig ned for Kongen paa sit Ansigt til Jorden.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Og Nathan sagde: Min Herre Konge, har du sagt: Adonia skal være Konge efter mig, og han skal sidde paa min Trone?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 Thi han gik ned i Dag og slagtede Øksne og fedt Kvæg og Faar i Mangfoldighed, og han indbød alle Kongens Sønner og Høvedsmændene for Hæren og Abjathar, Præsten, og se, de æde og de drikke for hans Ansigt, og de sige: Kong Adonia leve!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 Men mig, som er din Tjener, og Zadok, Præsten, og Benaja, Jojadas Søn, og Salomo, din Tjener, indbød han ikke.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Mon denne Sag skulde være sket af min Herre Kongen? og du lod din Tjener ikke vide, hvo der skal sidde paa min Herre Kongens Trone efter ham.
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Og Kong David svarede og sagde: Kalder Bathseba til mig; og hun kom for Kongen og stod for Kongens Ansigt.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 Da svor Kongen og sagde: Saa vist som Herren lever, han som har forløst min Sjæl af al Angest:
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Ligesom jeg har tilsvoret dig ved Herren Israels Gud og sagt, at Salomo, din Søn, skal være Konge efter mig, og han skal sidde paa min Trone i mit Sted, saaledes vil jeg gøre paa denne Dag.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Da bøjede Bathseba sig med Ansigtet til Jorden og kastede sig ned for Kongen, og hun sagde: Min Herre, Kong David, leve i Evighed!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Og Kong David sagde: Kalder mig Zadok, Præsten, og Nathan, Profeten, og Benaja, Jojadas Søn; og de kom ind for Kongens Ansigt.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Da sagde Kongen til dem: Tager med eder eders Herres Tjenere, og lader min Søn Salomo ride paa den Mulæselinde, som hører mig til, og fører ham ned til Gihon.
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 Og Zadok, Præsten, og Nathan, Profeten, skulle der salve ham til Konge over Israel; og I skulle blæse i Trompeten og sige: Kong Salomo leve!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Og drager op efter ham, saa skal han komme og sidde paa min Trone, og han skal være Konge i mit Sted; thi jeg har budet ham at være Fyrste over Israel og over Juda.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Da svarede Benaja, Jojadas Søn, Kongen og sagde: Amen! saa sige Herren, min Herre Kongens Gud:
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 Saasom Herren har været med min Herre Kongen, saa være han med Salomo, og gøre hans Trone større end min Herres, Kong Davids Trone!
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Da gik Zadok, Præsten, og Nathan, Profeten, og Benaja, Jojadas Søn, og de Krethi og de Plethi ned og satte Salomo paa Kong Davids Mulæselinde, og de førte ham til Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Og Zadok, Præsten, tog Oliehornet af Paulunet og salvede Salomo; og de blæste i Trompeten, og alt Folket sagde: Kong Salomo leve!
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 Og alt Folket drog op efter ham, og Folket blæste paa Fløjter og glædede sig med en stor Glæde, saa at Jorden revnede af deres Skrig.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Og Adonia hørte det, og alle de indbudne, som vare hos ham, og de havde endt Maaltidet; og Joab hørte Trompetens Lyd og sagde: Hvorfor det Raab i den støjende Stad?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 Der han endnu talede, se, da kom Jonathan, Præsten Abjathars Søn, og Adonia sagde: Kom, thi du er en duelig Mand og fører et godt Budskab.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Og Jonathan svarede og sagde til Adonia: Ja, vor Herre, Kong David, har gjort Salomo til Konge.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 Og Kongen sendte Zadok, Præsten, og Nathan, Profeten, og Benaja, Jojadas Søn, og de Krethi og de Plethi med ham, og de lode ham ride paa Kongens Mulæselinde.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 Og Zadok, Præsten, og Nathan, Profeten, salvede ham til Konge i Gihon og droge derfra glade op, saa at Staden er sat i Bevægelse derved; det er det Raab, som I have hørt.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Dertilmed sidder Salomo paa den kongelige Trone.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 Og Kongens Tjenere kom ogsaa at velsigne vor Herre, Kong David, og sagde: Din Gud gøre Salomos Navn bedre end dit Navn og gøre hans Trone større end din Trone! og Kongen tilbad paa Sengen.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Og Kongen sagde ogsaa saaledes: Lovet være Herren, Israels Gud, som i Dag har givet en, som sidder paa min Trone, at mine Øjne se det!
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Da bleve alle, som vare indbudne af Adonia, forfærdede og stode op; og de gik hver sin Vej.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Og Adonia frygtede for Salomos Ansigt, og han stod op og gik bort og tog fat paa Alterets Horn.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 Og det blev Salomo kundgjort og sagt: Se, Adonia frygter for Kong Salomo, og se, han tager fat paa Alterets Horn og siger: Kong Salomo skal sværge mig paa denne Dag, at han ikke vil dræbe sin Tjener med Sværd.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Og Salomo sagde: Dersom han vil være en redelig Mand, skal der ikke falde et af hans Haar paa Jorden; men om der bliver fundet ondt hos ham, da skal han dø.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Og Kong Salomo sendte hen, og de hentede ham ned fra Alteret, og han kom og bøjede sig ned for Kong Salomo; og Salomo sagde til ham: Gak til dit Hus.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”