< 1 Korinterne 11 >
1 Vorder mine Efterfølgere, ligesom ogsaa jeg er Kristi!
Ku yi koyi da ni, kamar yadda nake koyi da Almasihu.
2 Men jeg roser eder, fordi I komme mig i Hu i alt og holde fast ved Overleveringerne, saaledes som jeg har overleveret eder dem.
Yanzu ina yaba maku ne, don kuna tunawa da ni cikin abu duka. Ina kuma yaba maku wajen bin al'adun da na ba ku daidai yadda na ba ku.
3 Men jeg vil, at I skulle vide, at Kristus er enhver Mands Hoved; men Manden er Kvindens Hoved; men Gud er Kristi Hoved.
Amma fa ina son ku fahimta da cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace mutumin ne, shugaban Almasihu Allah ne.
4 Hver Mand, som beder eller profeterer med tildækket Hoved, beskæmmer sit Hoved.
Kuma duk mutumin da ya yi addu'a ko annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa.
5 Men hver Kvinde, som beder eller profeterer med utildækket Hoved, beskæmmer sit Hoved; thi det er lige det samme, som var hun raget.
Amma duk macen da ta yi addu'a ko annabci kanta a bude, ta wulakanta shugabanta. Gama yayi dai dai da idan tayi aski.
6 Thi naar en Kvinde ikke tildækker sig, saa lad hende ogsaa klippe sit Haar af; men er det usømmeligt for en Kvinde at klippes eller rages, da tildække hun sig!
Gama idan mace ba zata rufe kanta ba, to ta yanke gashinta ya zama gajere. Idan abin kunya ne mace ta yanke gashinta ko ta aske kanta, bari ta rufe kanta.
7 Thi en Mand bør ikke tildække sit Hoved, efterdi han er Guds Billede og Ære; men Kvinden er Mandens Ære.
Bai kamata na miji ya rufe kansa ba, tun da yake shi siffa ne da daukakar Allah. Amma mace daukakar namiji ce.
8 Mand er jo ikke af Kvinde, men Kvinde af Mand.
Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba. A maimako, matar daga jikin namiji take.
9 Ej heller er jo Mand skabt for Kvindens Skyld, men Kvinde for Mandens Skyld.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba. A maimako, an halicci mace don namiji.
10 Derfor bør Kvinden have et Ærbødighedstegn paa Hovedet for Englenes Skyld.
Shi ya sa mace za ta kasance da alamar iko a kanta, saboda mala'iku.
11 Dog er hverken Kvinde uden Mand eller Mand uden Kvinde i Herren.
Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba.
12 Thi ligesom Kvinden er af Manden, saaledes er ogsaa Manden ved Kvinden; men alt sammen er det af Gud.
Kamar yadda mace take daga namiji, haka ma namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke.
13 Dømmer selv: Er det sømmeligt, at en Kvinde beder til Gud med utildækket Hoved?
Ku hukunta da kanku: Daidai ne mace ta yi addu'a ga Allah kanta a bude?
14 Lærer ikke ogsaa selve Naturen eder, at naar en Mand bærer langt Haar, er det ham en Vanære,
Ashe, ko dabi'a bata nuna maku cewa abin kunya ne namiji, ya kasance da dogon gashi ba?
15 men naar en Kvinde bærer langt Haar, er det hende en Ære; thi det lange Haar er givet hende som et Slør.
Ba dabi'a ta koya maku cewa idan mace tana da dogon gashi, daukakar ta ne ba? Gama domin rufewa aka yi mata baiwar gashin.
16 Men har nogen Lyst til at trættes herom, da have vi ikke saadan Skik, og Guds Menigheder ej heller.
To idan wani yana da niyyaryin gardama game da wannan, mu dai bamu da wata al'adar, ikilisiyoyin Allah kuma haka.
17 Men idet jeg giver følgende Formaning, roser jeg ikke, at I komme sammen, ikke til det bedre, men til det værre.
Amma game da umarnin dake biye, ban yaba maku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin gaskiya ce.
18 For det første nemlig hører jeg, at naar I komme sammen i Menighedsforsamling, er der Splittelser iblandt eder; og for en Del tror jeg det.
Farko dai sa'adda kuke, taron ikklisiya, na ji har akwai rarrabuwa tsakaninku, har na fara amincewa da maganar.
19 Thi der maa endog være Partier iblandt eder, for at de prøvede kunne blive aabenbare iblandt eder.
Dole ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya gane wadanda suke amintattu a cikinku.
20 Naar I da komme sammen, er dette ikke at æde en Herrens Nadvere.
Domin, in kun taru a wuri daya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba!
21 Thi under Spisningen tager enhver sit eget Maaltid forud, og den ene hungrer, den anden beruser sig.
Ya yin da kuke ci, kowa na cin abincinsa ne kamin sauran Wani yana jin yunwa, wani kuma ya zarin ci, har ya bugu.
22 Have I da ikke Huse til at spise og drikke i? eller foragte I Guds Menighed og beskæmme dem, som intet have? Hvad skal jeg sige eder? skal jeg rose eder? I dette roser jeg eder ikke.
Baku da gidajen da zaku ci ku sha, kuna raina ikkilisiyar Allah, kuna kuma wulakanta wa wadanda basu da komai? To, me zan ce maku? Yaba maku zan yi? Ba zan yaba maku ba akan wannan.
23 Thi jeg har modtaget fra Herren, hvad jeg ogsaa har overleveret eder: At den Herre Jesus i den Nat, da han blev forraadt, tog Brød,
Amma abin da na karba a gun Ubangiji shi nake baku cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi ya dauki gurasa.
24 takkede og brød det og sagde: „Dette er mit Legeme, som er for eder; gører dette til min Ihukommelse!‟
Bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “wanna shi ne jikina wanda yake saboda ku, ku yi domin tunawa da ni.”
25 Ligesaa tog han ogsaa Kalken efter Aftensmaaltidet og sagde: „Denne Kalk er den nye Pagt i mit Blod; gører dette, saa ofte som I drikke det, til min Ihukommelse!‟
Ta wannan hanya kuma, sai ya dauki kokon, ya ce, “kokon nan na sabon alkawari ne, da aka tabbatar da shi da cikin jinina. Ku yi haka kuna sha don tunawa da ni.”
26 Thi saa ofte, som I æde dette Brød og drikke Kalken, forkynde I Herrens Død, indtil han kommer.
Duk sa'adda kuke cin gurasar nan, kuna kuma sha cikin kokon nan, kuna bayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.
27 Derfor, den, som æder Brødet eller drikker Herrens Kalk uværdigt, paadrager sig Skyld over for Herrens Legeme og Blod.
Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a cikin kokon nan, na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa.
28 Men hvert Menneske prøve sig selv, og saaledes æde han af Brødet og drikke af Kalken!
Sai kowa ya fara auna kansa, kafin ya ci gurasar, ya kuma sha a cikin kokon nan.
29 Thi den, som æder og drikker, æder og drikker sig selv en Dom til, naar han ikke agter paa Legemet.
In kowa ya ci, ya sha ba tare da rarrabewa da jikin Ubangiji ba, lalle ya jawowa kansa hukunci, ta wurin ci da sha da ya yi.
30 Derfor ere mange skrøbelige og sygelige iblandt eder, og en Del sover hen.
Shi ya sa da yawa a cikin ku suke raunana, kuma suna fama da rashin lafiya, har ma wasun ku da dama suka yi barci.
31 Men dersom vi bedømte os selv, bleve vi ikke dømte.
Amma, in mun auna kanmu, ba a za a hukunta mu ba.
32 Men naar vi dømmes, tugtes vi af Herren, for at vi ikke skulle fordømmes med Verden.
In kuwa Ubangiji ne ya ke hukunta mu, To, muna horuwa ke nan, don kada a kayar damu tare da duniya.
33 Derfor, mine Brødre! naar I komme sammen til Maaltid, da venter paa hverandre!
Saboda haka, ya ku 'yan'uwana, idan kuka tattaru don cin abinci, sai ku jira juna.
34 Naar nogen hungrer, han spise hjemme, for at I ikke skulle komme sammen til Dom. Men det øvrige skal jeg forordne, naar jeg kommer.
Idan kuwa wani yana jin yunwa, ya ci a gida, kada ya zama taronku ya jawo maku hukunci. Batun sauran abubuwan da kuka rubuta kuwa, zan ba da umarni a kai sa'ad da na zo.