< Første Krønikebog 19 >

1 Og det skete derefter, at Nahas, Ammons Børns Konge, døde, og hans Søn blev Konge i hans Sted.
Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Da sagde David: Jeg vil gøre Miskundhed imod Hanon, Nahas Søn, thi hans Fader gjorde Miskundhed imod mig; og David sendte Bud at lade ham trøste over hans Fader, og Davids Tjenere kom til Ammons Børns Land, til Hanon, for at trøste ham.
Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
3 Da sagde Ammons Børns Fyrster til Hanon: Mon David i dine Øjne ærer din Fader ved det han sender dig Trøstere? mon hans Tjenere ikke ere komne til dig for at udforske og at omstyrte og at udspejde Landet?
sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
4 Da tog Hanon Davids Tjenere og lod dem rage og skar Halvdelen af deres Klæder indtil Skrævet og lod dem fare.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
5 Og nogle gik og gave David det til Kende om de Mænd; da sendte han dem et Bud i Møde, thi Mændene vare saare forhaanede, og Kongen lod sige: Bliver i Jeriko, indtil eders Skæg vokser, og kommer da tilbage!
Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
6 Der Ammons Børn saa, at de havde gjort sig forhadte for David, da sendte Hanon og Ammons Børn tusinde Centner Sølv for at leje sig fra Mesopotamien og fra Syria-Maaka og fra Zoba Vogne og Ryttere.
Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
7 Og de lejede sig to og tredive Tusinde Vognkæmpere og Kongen af Maaka og hans Folk, og de kom og lejrede sig lige for Medba; og Ammons Børn samlede sig fra deres Stæder og kom til Striden.
Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
8 Der David hørte det, da udsendte han Joab og de vældiges hele Hær.
Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
9 Og Ammons Børn droge ud og opstillede deres Slagorden foran Indgangen til Staden, men Kongerne, som vare komne, stillede særskilt paa Marken.
Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
10 Der Joab saa, at Krigen truede ham for og bagfra, da udvalgte han nogle af alle de udvalgte i Israel og opstillede sig imod Syrerne.
Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
11 Og det øvrige Folk gav han under sin Broder Abisajs Haand, og de opstillede sig imod Ammons Børn.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
12 Og han sagde: Dersom Syrerne blive mig for stærke, da skal du være mig til Hjælp; men dersom Ammons Børn blive dig for stærke, da vil jeg hjælpe dig.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
13 Vær frimodig, og lader os vise os frimodige for vort Folk og for vor Guds Stæder; men Herren gøre, hvad som godt er for hans Øjne.
Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
14 Da drog Joab frem og det Folk, som var hos ham, til Striden imod Syrerne; og disse flyede for hans Ansigt.
Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
15 Der Ammons Børn saa, at Syrerne flyede, da flyede de og for Abisaj, hans Broders, Ansigt, og kom til Staden; og Joab kom til Jerusalem.
Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
16 Og der Syrerne saa, at devare slagne for Israels Ansigt, da sendte de Bud og lode de Syrer, som vare paa hin Side Floden, rykke ud, og Sofak, Hadad-Esers Stridshøvedsmand, anførte dem.
Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
17 Der det blev David tilkendegivet, da samlede han hele Israel og drog over Jordanen, og han kom til dem og stillede sig imod dem, og David stillede sig i Slagorden imod Syrerne, og de strede med ham.
Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
18 Men Syrerne flyede for Israels Ansigt, og David ihjelslog af Syrerne syv Tusinde Vognkæmpere og fyrretyve Tusinde Fodfolk, ligeledes dræbte han Sofak, Stridshøvedsmanden.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
19 Der Hadad-Esers Tjenere saa, at de vare slagne for Israels Ansigt, da gjorde de Fred med David og tjente ham; og Syrerne vilde ikke ydermere hjælpe Ammons Børn.
Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.

< Første Krønikebog 19 >