< Første Krønikebog 18 >
1 Og det skete derefter, at David slog Filisterne og ydmygede dem, og han tog Gat og dens tilliggende Byer af Filisternes Haand.
Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
2 Han slog og Moabiterne, og Moabiterne bleve Davids Tjenere og bragte ham Skænk.
Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
3 David slog og Hadad-Eser, Kongen af Zoba, ved Hamat, der han drog hen at vende sin Haand imod Floden Frat.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
4 Og David tog fra ham tusinde Vogne og syv Tusinde Ryttere og tyve Tusinde Fodfolk, og David lammede alle Vognhestene, og han lod kun hundrede Heste blive tilovers af dem.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
5 Men Syrerne fra Damaskus kom for at hjælpe Hadad-Eser, Kongen af Zoba, og David slog af Syrerne to og tyve Tusinde Mand.
Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
6 Og David lagde Besætning udi Syrien i Damaskus, og Syrerne bleve Davids Tjenere og bragte ham Skænk, og Herren frelste David, i hvor han drog hen.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
7 Og David tog de Guldskjolde, som vare hos Hadad-Esers Tjenere, og førte dem til Jerusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
8 Og fra Tibehat og fra Kun, Hadad-Esers Stæder, tog David saare meget Kobber; deraf gjorde Salomo Kobberhavet og Støtterne og Kobberkarrene.
Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
9 Og der Thou, Kongen af Hamat, hørte, at David havde slaget hele Hadad-Esers, Kongen af Zobas, Hær,
Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
10 da sendte han sin Søn Hadoram til Kong David for at hilse ham og at velsigne ham, fordi han havde stridt imod Hadad-Eser og slaget ham; thi Hadad-Eser førte stedse Krig imod Thou; og han havde alle Haande Guldkar og Sølvkar og Kobberkar med sig.
sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
11 Ogsaa dem helligede Kong David for Herren, tillige med det Sølv og Guld, som han havde taget fra alle Hedninger, fra Edom og fra Moab og fra Ammons Børn og fra Filisterne og fra Amalek.
Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
12 Og Abisaj, Zerujas Søn, slog Edomiterne i Saltdalen, atten Tusinde.
Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
13 Og han lagde Besætning i Edom, og alle Edomiterne bleve Davids Tjenere; og Herren frelste David, i hvor han drog hen.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
14 Saa var David Konge over hele Israel, og han gjorde Ret og Retfærdighed for alt sit Folk.
Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
15 Og Joab, Zerujas Søn, var over Krigshæren, og Josafat, Ahiluds Søn, var Historieskriver.
Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
16 Og Zadok, Ahitubs Søn, og Abimelek, Abjathars Søn, vare Præster, og Sausa var Skriver.
Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
17 Og Benaja, Jojadas Søn, var over de Krethi og de Plethi; og Davids Sønner vare de første ved Kongens Haand.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.