< Første Krønikebog 14 >

1 Og Hiram, Kongen af Tyrus, sendte Bud til David med Cedertræ og Murmestre og Tømmermestre for at bygge ham et Hus.
To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
2 Og David fornam, at Herren havde stadfæstet ham til Konge over Israel; thi hans Rige blev overmaade ophøjet for hans Folks Israels Skyld.
Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
3 Og David tog endnu Hustruer i Jerusalem, og David avlede endnu Sønner og Døtre.
A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
4 Og disse vare deres Navne, som bleve ham fødte i Jerusalem: Sammua og Sobab, Nathan og Salomo
Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
5 og Jibkar og Elisua og Elifelet
Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
6 og Noga og Nefeg og Jafla
Noga, Nefeg, Yafiya,
7 og Elisama og Beeljada og Elifelet.
Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
8 Og der Filisterne hørte, at David var salvet til Konge over hele Israel, da droge alle Filisterne op for at søge efter David; der David hørte det, da drog han ud imod dem.
Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
9 Og Filisterne kom og udbredte sig i Refaims Dal.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
10 Og David spurgte Gud ad og sagde: Skal jeg drage op imod Filisterne? og vil du give dem i min Haand? Og Herren sagde til ham: Drag op, thi jeg vil give dem i din Haand.
sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
11 Og der de droge op til Baal-Perazim, da slog David dem der, og David sagde: Gud har brudt igennem mine Fjender ved min Haand, ligesom Vandet bryder igennem; derfor kaldte man det samme Steds Navn Baal-Perazim.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
12 Og de efterlode deres Guder der; og David bød, og de bleve opbrændte med Ild.
Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
13 Og Filisterne bleve endnu ved og udbredte sig i Dalen.
Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
14 Og David adspurgte Gud ydermere, og Gud sagde til ham: Du skal ikke drage op efter dem, men vend dig fra dem, at du kan komme til dem tværs over for Morbærtræerne.
sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
15 Og det skal ske, naar du hører en Lyd af en Skriden hen over Morbærtræernes Toppe, da skal du drage ud til Striden; thi Gud er udgangen for dit Ansigt at slaa Filisternes Lejr.
Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
16 Og David gjorde, som Gud havde befalet ham, og de sloge Filisternes Lejr fra Gibeon og indtil Geser.
Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
17 Og Davids Navn kom ud i alle Landene, og Herren lod Frygt for ham komme over alle Hedninger.
Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.

< Første Krønikebog 14 >