< Første Krønikebog 11 >

1 Da samledes hele Israel til David i Hebron og sagde: Se, vi ere dine Ben og dit Kød.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 Ogsaa tilforn, endog der Saul var Konge, har du ført Israel ud og ind; saa har og Herren din Gud sagt til dig: Du skal føde mit Folk Israel, og du skal være en Fyrste over mit Folk Israel.
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 Og alle Israels Ældste kom til Kongen i Hebron, og David gjorde en Pagt med dem i Hebron for Herrens Ansigt, og de salvede David til Konge over Israel efter Herrens Ord ved Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 Og David og hele Israel drog hen til Jerusalem, det er Jebus; og Jebusiterne vare der Landets Indbyggere.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 Og Indbyggerne i Jebus sagde til David: Du skal ikke komme herind; men David indtog Zions Befæstning, det er Davids Stad.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 Og David sagde: Hvo som helst der først slaar Jebusiterne, skal være en Øverste og Høvedsmand; saa steg Joab, Zerujas Søn, først op og blev Øverste.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 Og David boede i Befæstningen, derfor kaldte man den Davids Stad.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 Og han byggede Staden deromkring, fra Milla og rundt omkring; og Joab udbedrede det øvrige af Byen.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 Og David gik stedse frem og blev stor, og den Herre Zebaoth var med ham.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Og disse ere de Øverste iblandt de vældige, som David havde, som holdt mandeligen med ham i hans Regering tillige med hele Israel, saa at de gjorde ham til Konge efter Herrens Ord over Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 Og dette er Tallet paa de vældige, som David havde: Jasobeam, Hakmonis Søn, en Øverste for Høvedsmændene, han svingede sit Spyd imod tre Hundrede, som bleve ihjelslagne paa en Gang.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 Og efter ham var Eleasar, Dodos Søn, Ahohiten, han var iblandt de tre vældige.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 Han var med David i Pasdammin, der Filisterne vare samlede der til Striden, og der var et Stykke Ager fuldt med Byg, og Folket flyede for Filisternes Ansigt.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 Og de stillede sig midt paa det Stykke og reddede det og sloge Filisterne, og Herren gjorde en stor Frelse.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Og tre af de tredive ypperste droge ned til David ved Klippen til Hulen ved Adullam; men Filisternes Lejr havde lejret sig i Refaims Dal.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 Og David var da i Befæstningen, og Filisternes Besætning var da i Bethlehem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 Og David fik Lyst og sagde: Hvo vil give mig Vand at drikke af den Brønd i Bethlehem, som er ved Porten?
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Da brøde de tre ind i Filisternes Lejr og droge Vand af den Brønd i Bethlehem, som var ved Porten, og toge det op og bragte det til David; men David vilde ikke drikke det, men udøste det for Herren.
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 Og han sagde: Min Gud lade det være langt fra mig at gøre dette; skulde jeg drikke disse Mænds Blod, da de have sat deres Liv i Fare? thi med Livsfare have de bragt det hid; og han vilde ikke drikke det; dette gjorde de tre vældige.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Og Abisaj, Joabs Broder, var den ypperste iblandt de tre, og han svingede sit Spyd imod tre Hundrede, som bleve ihjelslagne; og han var navnkundig iblandt de tre.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Af de tre var han herligere end de to, derfor blev han deres Høvedsmand; men han naaede ikke de første tre.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaja, Jojadas Søn, en stridbar Mands Søn, mægtig i Gerninger, fra Kabzeel, han slog to Løvehelte af Moabiterne, og han gik ned og slog en Løve midt i en Brønd en Dag, da der var Sne.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 Og han slog en ægyptisk Mand, en Mand, fem Alen høj, og Ægypteren havde et Spyd i Haanden som en Væverstang; men han gik ned imod ham med en Kæp, og han rev Spydet af Ægypterens Haand og slog ham ihjel med hans eget Spyd.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Dette gjorde Benaja, Jojadas Søn, og han var navnkundig iblandt de tre vældige.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Se, han var mere æret end de tredive, dog naaede han ikke de tre; og David satte ham i sit Raad.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Men de vældige i Hærene vare: Asael, Joabs Broder; Elhanan, Dodos Søn af Bethlehem;
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Sammoth, Haroriten; Helez, Peloniten;
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira, Ikkes Søn, Thekoiten; Abieser, Anathothiten;
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibekaj, Husathiten; Haj, Ahohiten;
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharaj, Netofathiten; Heled, Baenas Søn, Netofathiten;
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithaj, Ribajs Søn, af Benjamins Børns Gibea; Benaja, Pireathoniten;
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Huraj fra Dalene ved Gaas; Abiel, Arbathiten;
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Asmaveth, Baharumiten; Eljakbar, Saalboniten;
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 Hasems, Gisonitens, Børn; Jonathan, Sages Søn, Harariten;
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam, Sakars Søn, Harariten; Elifal, Urs Søn;
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hefer, Makerathiten; Ahia, Peloniten;
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro, Karmeliten; Naeraj, Esbajs Søn;
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joel, Nathans Broder; Mibkar, Geris Søn;
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek, Ammoniten; Naheraj, Berothiten, Joabs, Zerujas Søns, Vaabendrager;
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira, Jithriten; Gareb, Jithriten;
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Uria, Hethiten; Sabad, Ahelajs Søn;
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina, Sisas Søn, Rubeniten, Rubeniternes Øverste, og tredive foruden ham;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan, Maakas Søn, og Josafat, Mithniten;
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Usia, Asthratiten; Sama og Jejel, Hotams, Aroeritens, Sønner;
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jedial, Simris Søn, og Joha, hans Broder, Thiziten;
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel af Maheviterne; og Jeribaj og Josavja, Elnaams Sønner; og Jitma, Moabiten;
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel og Obed og Jaesiel af Mezobaja.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< Første Krønikebog 11 >