< Lukáš 7 >

1 Když Ježíš skončil kázání k lidem, šel do Kafarnaum.
Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
2 Tam žil jeden římský důstojník, který vlastnil otroka. Velice si ho cenil, a proto těžce nesl, když otrok smrtelně onemocněl.
A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
3 Důstojník se doslechl o Ježíšovi a poslal k němu židovské starší s prosbou, aby přišel a otroka zachránil.
Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
4 Ti se vydali za Ježíšem a naléhali: „Ten muž si zaslouží tvou pomoc.
Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
5 Má rád náš národ a dokonce nám dal postavit synagogu.“
gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
6 Ježíš s nimi šel. Když už byli nedaleko jeho domu, poslal k němu důstojník své přátele se vzkazem: „Pane, neobtěžuj se tolik, nezasloužím si, abys mne poctil svou návštěvou.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
7 Jako pohan jsem se ani neodvážil jít za tebou osobně. Stačí, když řekneš slovo, a můj otrok se určitě uzdraví.
Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
8 Vždyť i já musím splnit rozkaz svých nadřízených a moji podřízení se musí zase podrobit mým povelům. Řeknu-li vojákovi: ‚Jdi!‘tak jde, a řeknu-li druhému: ‚Přijď!‘tak přijde. Poručím-li svému otrokovi: ‚Udělej toto!‘tedy to udělá.“
Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
9 Ježíš byl těmi slovy velmi udiven a řekl svým průvodcům: „S tak velkou vírou jsem se nesetkal u žádného Žida.“
Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
10 Když se poslové vrátili do domu římského důstojníka, byl již otrok zdráv.
Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
11 Brzy nato se Ježíš odebral do města Naim. Jeho žáci a mnozí další lidé ho doprovázeli.
Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
12 V blízkosti městské brány potkali pohřební průvod. Jedna vdova pochovávala svého jediného syna. K pohřbu se sešlo hodně lidí.
Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
13 Když Ježíš spatřil tu vdovu, bylo mu jí velice líto a řekl: „Neplač!“
Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
14 Pak přistoupil blíže, dotkl se már a zastavil průvod. „Mládenče, vstaň!“zvolal.
Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
15 Tu se mrtvý posadil a promluvil. Tak Ježíš vrátil matce syna.
Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
16 Počáteční zděšení okolostojících vystřídala radost a začali chválit Boha: „Velký prorok přišel mezi nás! Bůh navštívil svůj lid.“
Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
17 Zpráva o této události se rozšířila po celém Judsku a okolí.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
18 O tom všem vyprávěli učedníci Jana Křtitele svému učiteli.
Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
19 Jan poslal dva z nich za Ježíšem, aby se zeptali: „Jsi Mesiáš, anebo máme čekat ještě někoho jiného!“
ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
20 Když přišli s tou otázkou, Ježíš právě uzdravoval nemocné, všelijak postižené, osvobozoval spoutané duševními nemocemi, mnohým slepým vracel zrak.
Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
22 Poslům odpověděl: „Jděte zpět k Janovi a řekněte mu, co jste viděli a slyšeli: slepí vidí, chromí chodí, hluší slyší, mrtví ožívají a těm, kteří nic nemají, nabízí Bůh podíl ve svém království.
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
23 Šťasten je každý, kdo mne neodmítne.“
Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
24 Když poslové odešli, začal Ježíš mluvit ke shromážděným lidem o Janu Křtiteli: „Když jste chodili za mužem, který strávil život v pustinách, koho jste očekávali? Rákos, který se otočí podle větru?
Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
25 Nebo jste chtěli vidět člověka v přepychových šatech? Takoví jsou jen v palácích.
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
26 Chtěli jste slyšet proroka? Ano, poznali jste někoho ještě většího než proroka.
Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
27 Jan je ten, o němž je napsáno: ‚Posílám svého posla před tebou, aby ti připravil cestu.‘
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
28 Jan dostal nejvyšší úkol ze všech lidí: oznámit, že Kristus přichází! A přece i ten nejnepatrnější, kdo se dočkal a uvěřil, byl poctěn více než Jan.
Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
29 Víte, že Janovi posluchači – a byli mezi nimi i lidé s všelijakou pověstí – přijali Jana jako Božího posla a dali se proto od něho pokřtít.
(Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
30 Farizejové a znalci zákona však Janův křest odmítli, protože nepochopili, že i oni potřebují Boží odpuštění.“
Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
31 Ježíš pokračoval: „Komu se tak podobají?
Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
32 Jsou nespokojení a náladoví jako děti, které si hrají na návsi chvíli na svatbu, chvíli na pohřeb a vzájemně si vyčítají: ‚Pískali jsme vám, a vy jste netancovali. A pak jsme vám zase smutně zpívali, a vy jste neplakali.‘
Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
33 Když se Jan Křtitel postil a nepil víno, říkali jste, že je fanatik,
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
34 a když Syn člověka jí a pije, říkáte pohrdlivě: ‚Podívejte se na toho žrouta a pijana, který se přátelí i se zrádci národa a s kdejakou sebrankou.‘
Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
35 Ale kdo přijme Boží moudrost, ten tomu porozumí.“
Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
36 Jeden farizej pozval Ježíše na oběd. Ten přišel a stoloval s ním.
To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
37 V tom městě žila také žena, která měla špatnou pověst. Když slyšela, že Ježíš je na návštěvě u farizeje Šimona, vzala alabastrovou nádobku s drahocenným vonným olejem a šla tam.
Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
38 Poklekla k Ježíšovým nohám, smáčela mu je slzami, utírala svými vlasy, líbala je a potírala vonným olejem.
ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
39 Když to viděl farizej, který Ježíše pozval, myslel si: „Kdyby to byl prorok, věděl by, co je to za ženu, a nedovolil by, aby se ho taková hříšnice vůbec dotkla.“
Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
40 Tu ho Ježíš oslovil: „Rád bych se tě, Šimone, na něco zeptal.“„Prosím, jen mluv, “řekl Šimon.
Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
41 „Jeden věřitel měl dva dlužníky. První mu byl dlužen pět set stříbrných, druhý padesát.
Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
42 Když však ani jeden z nich nemohl zaplatit, věřitel odpustil dluh oběma. Co myslíš, který z nich ho bude mít víc rád?“
Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
43 Šimon odpověděl: „Mám za to, že ten, kterému více prominul.“„Správně, “řekl Ježíš.
Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
44 Pak ukázal na ženu u svých nohou a pověděl Šimonovi: „Podívej se na tu ženu. Přišel jsem do tvého domu a ty jsi mi nedal umýt nohy, jak je zvykem; tato žena mi je umyla svými slzami a vytřela svými vlasy.
Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
45 Na uvítanou jsi mne jako hostitel nepolíbil, ale tato žena mi nepřestává líbat nohy.
Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
46 Nepotřel jsi mi hlavu olejem, ale tato žena nelitovala drahocenného oleje na mé nohy.
Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
47 Je to jako s těmi dlužníky: velký hřích je jí odpuštěn a to se projevuje na lásce, kterou mi prokazuje. Kdo si myslí, že odpuštění nepotřebuje, pak málo miluje.“
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48 Potom se obrátil k ženě: „Tvoje hříchy jsou ti odpuštěny.“
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49 Když si ostatní hosté říkali mezi sebou: „Co je to za člověka, že si troufá odpouštět hříchy?“
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50 uklidnil ji: „Tvoje víra tě zachránila, jdi pokojně domů.“
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”

< Lukáš 7 >