< Zjevení Janovo 1 >
1 Zjevení Ježíše Krista, kteréž dal jemu Bůh, aby ukázal služebníkům svým, které věci měly by se díti brzo, on pak zjevil, poslav je skrze anděla svého, služebníku svému Janovi,
Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
2 Kterýž osvědčil slovo Boží a svědectví Jezukristovo, a cožkoli viděl.
wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
3 Blahoslavený, kdož čte, i ti, kteříž slyší slova proroctví tohoto a ostříhají toho, což napsáno jest v něm; nebo čas blízko jest.
Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
4 Jan sedmi církvím, kteréž jsou v Azii: Milost vám a pokoj od toho, Jenž jest, a Kterýž byl, a Kterýž přijíti má, a od sedmi Duchů, kteříž před obličejem trůnu jeho jsou,
Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
5 A od Ježíše Krista, jenž jest svědek věrný, ten prvorozený z mrtvých, a kníže králů země, kterýžto zamiloval nás a umyl nás od hříchů našich krví svou,
da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
6 A učinil nás krále a kněží Bohu a Otci svému, jemužto buď sláva a moc na věky věků. Amen. (aiōn )
ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn )
7 Aj, béře se s oblaky, a uzříť jej všeliké oko, i ti, kteříž ho bodli; a budou plakati pro něj všecka pokolení země, jistě, Amen.
“Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
8 Jáť jsem Alfa i Omega, počátek i konec, praví Pán, Kterýž jest, a Kterýž byl, a Kterýž přijíti má, ten všemohoucí.
“Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
9 Já Jan, kterýž jsem i bratr váš, i spoluúčastník v soužení, i v království, i v trpělivosti Ježíše Krista, byl jsem na ostrově, kterýž slove Patmos, pro slovo Boží a svědectví Ježíše Krista.
Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
10 A byl jsem u vytržení ducha v den Páně, i uslyšel jsem za sebou hlas veliký jako trouby,
A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
11 An mi dí: Já jsem Alfa i Omega, ten první i poslední, a řekl: Co vidíš, piš do knihy, a pošli sborům, kteříž jsou v Azii, do Efezu, a do Smyrny, a do Pergamu, a do Tyatiru, a do Sardy, a do Filadelfie, i do Laodicie.
wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
12 I obrátil jsem se, abych viděl ten hlas, kterýž mluvil se mnou, a obrátiv se, uzřel jsem sedm svícnů zlatých,
Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
13 A uprostřed sedmi svícnů podobného Synu člověka, oblečeného v dlouhé roucho a přepásaného na prsech pasem zlatým.
A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
14 Hlava pak jeho a vlasové byli bílí, jako bílá vlna, jako sníh, a oči jeho jako plamen ohně.
Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
15 Nohy pak jeho podobné mosazi, jako v peci hořící; a hlas jeho jako hlas vod mnohých.
Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
16 A měl v pravé ruce své sedm hvězd, a z úst jeho meč s obou stran ostrý vycházel; a tvář jeho jako slunce, když jasně svítí.
A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
17 A jakž jsem jej uzřel, padl jsem k nohám jeho, jako mrtvý. I položil ruku svou pravou na mne, řka ke mně: Neboj se. Já jsem ten první i poslední,
Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
18 A živý, ješto jsem byl mrtvý, a aj, živý jsem na věky věků. Amen. A mám klíče pekla i smrti. (aiōn , Hadēs )
Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn , Hadēs )
19 Napiš ty věci, kteréž jsi viděl, a kteréž jsou, a kteréž se mají díti potom.
“Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
20 Tajemství sedmi hvězd, kteréž jsi viděl v pravici mé, a sedm svícnů zlatých, jest toto: Sedm hvězd jsou andělé sedmi církví; a sedm svícnů, kteréžs viděl, jest těch sedm církví.
Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.