< Žalmy 83 >
1 Píseň a žalm Azafův. Bože, neodmlčujž se, nečiň se neslyše, aniž se upokojuj, ó Bože silný.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Nebo aj, nepřátelé tvoji se bouří, a ti, kteříž tě v nenávisti mají, pozdvihují hlavy.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Chytře tajné rady proti lidu tvému skládají, a radí se proti těm, kteréž ty skrýváš,
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Říkajíce: Poďte, a vyhlaďme je, ať nejsou národem, tak aby ani zpomínáno nebylo více jména Izraelova.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Jednomyslněť se na tom spolu snesli, i smlouvou se proti tobě zavázali,
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Stánkové Idumejští a Izmaelitští, Moábští a Agarenští,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebálští a Ammonitští, a Amalechitští, Filistinští s obyvateli Tyrskými.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Ano i Assyrští spojili se s nimi, jsouce na ruku synům Lotovým. (Sélah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Učiniž jim jako Madianským, jako Zizarovi, a jako Jabínovi při potoku Císon,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Kteříž jsou do konce vyhlazeni v Endor, a učiněni hnůj země.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Nalož s nimi a s vůdci jejich jako s Gorébem, jako s Zébem, jako s Zebahem, a jako s Salmunou, se všemi knížaty jejich.
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Neboť jsou řekli: Uvažme se dědičně v příbytky Boží.
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Můj Bože, učiň to, ať jsou jako chumelice, a jako stéblo před větrem.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Jakož oheň spaluje les, a jako plamen zapaluje hory,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 Tak ty je vichřicí svou stihej, a bouří svou ohrom je.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Naplň tváře jejich zahanbením, tak aby hledali jména tvého, Hospodine.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Nechať se hanbí a děsí na věčné časy, a ať potupu nesou a zahynou.
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 A tak ať poznají, že ty, kterýž sám jméno máš Hospodin, jsi nejvyšší nade vší zemí.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.