< Žalmy 80 >

1 Přednímu z kantorů na šošannim, žalm svědectví, Azafovi. Ó pastýři Izraelský, pozoruj, kterýž vodíš Jozefa jako stádo, kterýž sedíš nad cherubíny, ó zastkvějž se.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 Před Efraimem, Beniaminem a Manasse vzbuď moc svou, a přispěj k spasení našemu.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Ó Bože, navrať nás, a dejž, ať nám svítí oblíčej tvůj, a spaseni budeme.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 Hospodine Bože zástupů, dokudž se přísně stavěti budeš k modlitbám lidu svého?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 Nakrmil jsi je chlebem pláče, a dals jim vypiti slz míru velikou.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 Postavils nás k sváru sousedům našim, a nepřátelé naši aby sobě posměch z nás činili.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 Ó Bože zástupů, navrať nás, a dej, ať nám svítí oblíčej tvůj, a spaseni budeme.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 Ty jsi kmen vinný z Egypta přenesl, vyhnal jsi pohany, a vsadils jej.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 Uprázdnil jsi mu, a učinils, aby se vkořenil, i zemi naplnil.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 Přikryty jsou hory stínem jeho, a réví jeho jako nejvyšší cedrové.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 Vypustil ratolesti své až k moři, a až do řeky rozvody své.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 I pročež jsi rozbořil hradbu vinice, tak aby každý, kdož by tudy šel, trhati z ní mohl?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 Vepř divoký zryl ji, a zvěř polní spásla ji.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Ó Bože zástupů, obrať se již, popatř s nebe, viz a navštěv kmen vinný tento,
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 Vinici tu, kterouž štípila pravice tvá, a mladistvé réví, kteréž jsi zmocnil sobě.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 Popálenať jest ohněm a poroubána, od žehrání oblíčeje tvého hyne.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Budiž ruka tvá nad mužem pravice tvé, nad synem člověka, kteréhož jsi zmocnil sobě,
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 A neodstoupímeť od tebe; zachovej nás při životu, ať jméno tvé vzýváme.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 Hospodine Bože zástupů, navratiž nás zase, a dej, ať nám svítí oblíčej tvůj, a spaseni budeme.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Žalmy 80 >