< Žalmy 78 >

1 Vyučující, Azafovi. Pozoruj, lide můj, zákona mého, nakloňte uší svých k slovům úst mých.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Otevru v podobenství ústa svá, vypravovati budu přípovídky starobylé.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Co jsme slýchali i poznali, a co nám otcové naši vypravovali,
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Nezatajíme toho před syny jejich, kteříž budoucím potomkům svým vypravovati budou chvály Hospodinovy, ano i moc jeho a divné skutky jeho, kteréž činil.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Neboť jest vyzdvihl svědectví v Jákobovi, a zákon vydal v Izraeli, což přikázal otcům našim, aby v známost uvodili synům svým,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 Aby to poznal věk potomní, synové, kteříž se zroditi měli, a ti povstanouce, aby vypravovali dítkám svým,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Aby pokládali v Bohu naději svou, a nezapomínali se na skutky Boha silného, ale ostříhali přikázaní jeho,
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 Aby nebývali jako otcové jejich, pokolení zpurné a protivné, národ, kterýž nenapravil srdce svého, a nebyl věrný Bohu silnému duch jeho.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Jako synové Efraim zbrojní, ač uměle z lučiště stříleli, však v čas boje zpět se obrátili,
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Nebo neostříhali smlouvy Boží, a v zákoně jeho zpěčovali se choditi.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Zapomenuli se na činy jeho, a na divné skutky jeho, kteréž jim ukázal.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Před otci jejich činil divy v zemi Egyptské, na poli Soan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Rozdělil moře, a převedl je; učinil, aby stály vody jako hromada.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Vedl je ve dne v oblace, a každé noci v jasném ohni.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Protrhl skály na poušti, a napájel je jako z propastí velikých.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Vyvedl potoky z skály, a učinil, aby vody tekly jako řeky.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 A však vždy přičíněli hříchů proti němu, a popouzeli Nejvyššího na poušti.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 A pokoušeli Boha silného v srdci svém, žádajíce pokrmu podlé líbosti své.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 A mluvili proti Bohu, řkouce: Zdaliž bude moci Bůh silný připraviti stůl na této poušti?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Aj, udeřilť jest v skálu, a tekly vody, a řeky se rozvodnily. Zdali také bude moci dáti chleba? Zdali nastrojí masa lidu svému?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 A protož uslyšav Hospodin, rozhněval se, a oheň zažžen jest proti Jákobovi, a prchlivost vstoupila na Izraele,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Proto že se nedověřili Bohu, a neměli naděje v spasení jeho,
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Ačkoli rozkázal oblakům shůry, a průduchy nebeské otevřel,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 A dštil na ně mannou ku pokrmu, a obilé nebeské dával jim.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Chléb mocných jedl člověk, seslal jim pokrmů do sytosti.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Obrátil vítr východní u povětří, a přivedl mocí svou vítr polední.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 I dštil na ně masem jako prachem, a ptactvem pernatým jako pískem mořským.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Spustil je do prostřed vojska jejich, a všudy vůkol stanů jejich.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 I jedli, a nasyceni jsou hojně, a dal jim to, čehož žádali.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Ještě nevyplnili žádosti své, ještě pokrm byl v ústech jejich,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 A v tom prchlivost Boží připadla na ně, a zbil tučné jejich, a přední Izraelské porazil.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 S tím se vším vždy ještě hřešili, a nevěřili předivným skutkům jeho.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 A protož dopustil na ně, že marně skonali dny své, a léta svá s chvátáním.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Když je hubil, jestliže ho hledali, a zase k Bohu silnému hned na úsvitě se navraceli,
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Rozpomínajíce se na to, že Bůh byl skála jejich, a Bůh silný nejvyšší vykupitel jejich:
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 (Ačkoli mu s pochlebenstvím mluvili ústy svými, a jazykem svým lhali jemu.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 A srdce jejich nebylo upřímé před ním, aniž se věrně měli v smlouvě jeho),
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 On jsa milosrdný, odpouštěl nepravosti jejich, a nezahladil jich; častokrát odvracel hněv svůj, a nevzbuzoval vší zůřivosti své.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Nebo pamatoval, že jsou tělo, vítr, kterýž odchází, a nenavracuje se zase.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Kolikrát jsou ho dráždili na poušti, a k bolesti přivodili na pustinách.
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Týž i týž navracujíce se, pokoušeli Boha silného, a svatému Izraelskému cíle vyměřovali.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Nepamatovali na moc jeho, a na ten den, v kterémž je vysvobodil z ssoužení,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Když činil v Egyptě znamení svá, a zázraky své na poli Soan,
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Když obrátil v krev řeky a potoky jejich, tak že jich píti nemohli.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Dopustil na ně směsici žížal, aby je žraly, a žáby, aby je hubily.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 A dal chroustům úrody jejich, a úsilí jejich kobylkám.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Stloukl krupami réví jejich, a stromy fíkové jejich ledem.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Vydal krupobití na hovada jejich, a na dobytek jejich uhlí řeřavé.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Poslal na ně prchlivost hněvu svého, rozpálení, zůřivost i ssoužení, dopustiv na ně anděly zlé.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Uprostrannil stezku prchlivosti své, neuchoval od smrti duše jejich, ano i na hovada jejich mor dopustil.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 A pobil všecko prvorozené v Egyptě, prvotiny síly v staních Chamových.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Ale lid svůj vyvedl jako ovce, a vodil se s nimi jako s stádem po poušti.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Vodil je v bezpečnosti, tak že nestrašili, nepřátely pak jejich přikrylo moře,
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Až je přivedl ku pomezí svatosti své, na horu tu, kteréž dobyla pravice jeho.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Vyhnav před tváří jejich národy, způsobil to, aby jim na provazec dědictví jejich přišli, a aby přebývala v staních jejich pokolení Izraelská.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Však vždy předce pokoušeli a dráždili Boha nejvyššího, a svědectví jeho neostříhali.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Ale zpět odšedše, převráceně činili, jako i předkové jejich; uchýlili se jako mylné lučiště.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Nebo popouzeli ho výsostmi svými, a rytinami svými k horlení přivedli jej.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Slyšel Bůh, a rozhněval se, a u velikou ošklivost vzal Izraele,
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Tak že opustiv příbytek v Sílo, stánek, kterýž postavil mezi lidmi,
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Vydal v zajetí sílu svou, a slávu svou v ruce nepřítele.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Dal pod meč lid svůj, a na dědictví své se rozhněval.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Mládence jeho sežral oheň, a panny jeho nebyly chváleny.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Kněží jejich od meče padli, a vdovy jejich neplakaly.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Potom pak procítil Pán jako ze sna, jako silný rek, kterýž po víně sobě vykřikuje.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 A ranil nepřátely své po zadu, a u věčné pohanění je vydal.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Ačkoli pak pohrdl stánkem Jozefovým, a pokolení Efraimova nevyvolil,
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Však vyvolil pokolení Judovo, horu Sion, kterouž zamiloval.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 A vystavěl sobě, jako hrad vysoký, svatyni svou, jako zemi, kterouž utvrdil na věky.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 A vyvolil Davida služebníka svého, vzav jej od chlévů stáda.
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Když chodil za ovcemi březími, zavedl jej, aby pásl Jákoba, lid jeho, a Izraele, dědictví jeho.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Kterýž pásl je v upřímnosti srdce svého, a zvláštní opatrností rukou svých vodil je.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Žalmy 78 >