< Žalmy 72 >

1 Šalomounovi. Bože, soudy své králi dej, a spravedlnost svou synu královu,
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Aby soudil lid tvůj v spravedlnosti a chudé tvé v pravosti.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Hory přinesou pokoj lidu i pahrbkové v spravedlnosti.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Souditi bude chudé z lidu, a vysvobodí syny nuzného, násilníka pak potře.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Báti se budou tebe, dokudž slunce a měsíc trvati bude, od národu až do pronárodu.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Jako když sstupuje déšť na přisečenou trávu, a jako tiší déšťové skrápějící zemi:
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Tak zkvete ve dnech jeho spravedlivý, a bude hojnost pokoje, dokud měsíce stává.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Panovati bude od moře až k moři, a od řeky až do končin země.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Před ním skláněti se budou obyvatelé pustin vyprahlých, a nepřátelé jeho prach lízati budou.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Králové při moři a z ostrovů pocty mu přinesou, králové Šebejští a Sabejští dary obětovati budou.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Nadto klaněti se jemu budou všickni králové, všickni národové jemu sloužiti budou.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Nebo vytrhne nuzného, volajícího a nátisk trpícího, kterýž nemá spomocníka.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Smiluje se nad bídným a potřebným, a duše nuzných spasí.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Od lsti a násilí vysvobodí duši jejich; neboť jest drahá krev jejich před očima jeho.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Budeť dlouhověký, a dávati mu budou zlato Arabské, a ustavně za něj se modliti, na každý den jemu dobrořečiti budou.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Když se vrže hrst obilí do země na vrchu hor, klátiti se budou jako Libán klasové jeho, a kvésti budou měšťané jako byliny země.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Jméno jeho bude na věky; dokudž slunce trvá, děditi bude jméno jeho. A požehnání sobě dávajíce v něm všickni národové, budou ho blahoslaviti.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Požehnaný Hospodin Bůh, Bůh Izraelský, kterýž sám činí divné věci,
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 A požehnané jméno slávy jeho na věky. Budiž také naplněna slávou jeho všecka země, Amen i Amen.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Skonávají se modlitby Davidovy, syna Izai.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Žalmy 72 >