< Žalmy 14 >
1 Přednímu zpěváku, píseň Davidova. Říká blázen v srdci svém: Není Boha. Porušeni jsou, a ohavní v snažnostech; není, kdo by činil dobré.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
2 Hospodin s nebe popatřil na syny lidské, aby viděl, byl-li by kdo rozumný a hledající Boha.
Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 Všickni se odvrátili, napořád neužiteční učiněni jsou; není, kdo by činil dobré, není ani jednoho.
Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
4 Zdaliž nevědí všickni činitelé nepravosti, že zžírají lid můj, jako by chléb jedli? Hospodina pak nevzývají.
Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
5 Tehdáž se náramně strašiti budou; nebo Bůh jest v rodině spravedlivého.
Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
6 Radu chudého potupujete, ale Hospodin jest naděje jeho.
Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
7 Ó by z Siona dáno bylo spasení Izraelovi. Když Hospodin zase přivede zajaté lidu svého, plésati bude Jákob, a veseliti se Izrael.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!