< Žalmy 12 >
1 Přednímu kantoru k nízkému zpěvu, žalm Davidův. Spomoz, ó Hospodine; nebo se již nenalézá milosrdného, a vyhynuli věrní z synů lidských.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 Lež mluví jeden každý s bližním svým, rty úlisnými z srdce dvojitého řeči vynášejí.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 Ó by vyplénil Hospodin všeliké rty úlisné, a jazyk velikomluvný,
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 Kteříž říkají: Jazykem svým přemůžeme, mámeť ústa svá s sebou, kdo jest pánem naším?
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 Pro zhoubu chudých, pro úpění nuzných jižť povstanu, praví Hospodin, v bezpečnosti postavím toho, na nějž polečeno bylo.
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 Výmluvnosti Hospodinovy jsou výmluvnosti čisté, jako stříbro v hliněné peci přehnané a sedmkrát zprubované.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 Ty, Hospodine, jim spomáhati budeš, a ostříhati každého od národu tohoto až na věky.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 Vůkol a vůkol bezbožní se protulují, když takoví ničemní vyvýšeni bývají mezi syny lidskými.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.