< Príslovia 28 >

1 Utíkají bezbožní, ač jich žádný nehoní, ale spravedliví jako mladý lev smělí jsou.
Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
2 Pro přestoupení země mnoho knížat jejích, ale pro člověka rozumného a umělého trvánlivé bývá panování.
Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
3 Muž chudý, kterýž utiská nuzné, podoben jest přívalu zachvacujícímu, za čímž nebývá chleba.
Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
4 Kteří opouštějí zákon, chválí bezbožného, ale kteříž ostříhají zákona, velmi jsou jim na odpor.
Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
5 Lidé zlí nesrozumívají soudu, ti pak, kteříž hledají Hospodina, rozumějí všemu.
Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
6 Lepší jest chudý, kterýž chodí v upřímnosti své, než převrácený na kterékoli cestě, ačkoli jest bohatý.
Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
7 Kdo ostříhá zákona, jest syn rozumný; kdož pak s žráči tovaryší, hanbu činí otci svému.
Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
8 Kdo rozmnožuje statek svůj lichvou a úrokem, shromažďuje tomu, kdož by jej z milosti chudým rozděloval.
Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
9 Kdo odvrací ucho své, aby neslyšel zákona, i modlitba jeho jest ohavností.
In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
10 Kdo zavodí upřímé na cestu zlou, do jámy své sám vpadne, ale upřímí dědičně obdrží dobré.
Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
11 Moudrý jest u sebe sám muž bohatý, ale chudý rozumný vystihá jej.
Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
12 Když plésají spravedliví, velmi to pěkně sluší; ale když povstávají bezbožní, vyhledáván bývá člověk.
Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
13 Kdo přikrývá přestoupení svá, nepovede se jemu šťastně; ale kdož je vyznává a opouští, milosrdenství důjde.
Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
14 Blahoslavený člověk, kterýž se strachuje vždycky; ale kdož zatvrzuje srdce své, upadne ve zlé.
Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
15 Lev řvoucí a nedvěd hladovitý jest panovník bezbožný nad lidem nuzným.
Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
16 Kníže bez rozumu bývá veliký dráč, ale kdož v nenávisti má mrzký zisk, prodlí dnů.
Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
17 Èlověka, kterýž násilí činí krvi lidské, ani nad jamou, když utíká, žádný ho nezadrží.
Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
18 Kdo chodí upřímě, zachován bude, převrácený pak na kterékoli cestě padne pojednou.
Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
19 Kdo dělá zemi svou, nasycen bývá chlebem; ale kdož následuje zahalečů, nasycen bývá chudobou.
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
20 Muž věrný přispoří požehnání, ale kdož chvátá zbohatnouti, nebývá bez viny.
Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
21 Přijímati osobu není dobré; nebo mnohý pro kus chleba neprávě činí.
Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
22 Èlověk závistivý chvátá k statku, nic nevěda, že nouze na něj přijde.
Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
23 Kdo domlouvá člověku, potom spíše milost nalézá nežli ten, kterýž lahodí jazykem.
Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
24 Kdo loupí otce svého a matku svou, a říká, že to není žádný hřích, tovaryš jest vražedlníka.
Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
25 Vysokomyslný vzbuzuje svár, ale kdo doufá v Hospodina, hojnost míti bude.
Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
26 Kdo doufá v srdce své, blázen jest; ale kdož chodí moudře, pomůže sobě.
Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
27 Kdo dává chudému, nebude míti žádného nedostatku; kdož pak zakrývá oči své, bude míti množství zlořečení.
Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
28 Když povstávají bezbožní, skrývá se člověk; ale když hynou, rozmnožují se spravedliví.
Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.

< Príslovia 28 >