< Matouš 3 >
1 V těch pak dnech přišel Jan Křtitel, káže na poušti Judské,
A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
2 A řka: Pokání čiňte, nebo přiblížilo se království nebeské.
yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
3 Totoť jest zajisté ten Předchůdce předpověděný od Izaiáše proroka, řkoucího: Hlas volajícího na poušti: Připravujte cestu Páně, přímé čiňte stezky jeho.
Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Měl pak Jan roucho z srstí velbloudových a pás kožený okolo bedr svých, a pokrm jeho byl kobylky a med lesní.
Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
5 Tedy vycházeli k němu z Jeruzaléma a ze všeho Judstva, i ze vší krajiny ležící při Jordánu,
Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
6 A křtěni byli od něho v Jordáně, vyznávajíce hříchy své.
Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
7 Uzřev pak mnohé z farizeů a z saduceů, že jdou k jeho křtu, řekl jim: Pokolení ještěrčí, i kdo vám ukázal, kterak byste utéci měli budoucího hněvu?
Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Protož čiňte ovoce hodné pokání.
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
9 A nedomnívejte se, že můžete říkati sami u sebe: Otce máme Abrahama. Neboť pravím vám, že by mohl Bůh z kamení tohoto vzbuditi syny Abrahamovi.
Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
10 A jižť jest i sekera k kořenu stromů přiložena. Každý zajisté strom, kterýž nenese ovoce dobrého, vyťat a na oheň uvržen bývá.
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
11 Já křtím vás vodou ku pokání, ten pak, kterýž po mně přichází, jestiť mocnější nežli já, jehožto nejsem hoden obuvi nositi. Onť vás křtíti bude Duchem svatým a ohněm.
“Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
12 Jehožto věječka v ruce jeho, a vyčistíť humno své, a shromáždí pšenici svou do obilnice, ale plevy páliti bude ohněm neuhasitelným.
Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
13 Tehdy přišel Ježíš od Galilee k Jordánu k Janovi, aby také pokřtěn byl od něho.
Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
14 Ale Jan zbraňoval mu, řka: Mně jest potřebí, abych od tebe pokřtěn byl, a ty pak jdeš ke mně?
Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
15 A odpovídaje Ježíš, dí jemu: Dopusť tak; neboť tak sluší na nás, abychom plnili všelikou spravedlnost. Tedy dopustil jemu.
Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
16 A pokřtěn jsa Ježíš, vystoupil ihned z vody; a aj, otevřína jsou mu nebesa, a viděl Ducha Božího, sstupujícího jako holubici a přicházejícího na něj.
Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
17 A aj, zavzněl hlas s nebe řkoucí: Tentoť jest ten můj milý Syn, v němž mi se dobře zalíbilo.
Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”