< Matouš 22 >
1 I odpovídaje Ježíš, mluvil jim opět v podobenstvích, řka:
Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
2 Podobno jest království nebeské člověku králi, kterýž učinil svadbu synu svému.
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
3 I poslal služebníky své, aby povolali pozvaných na svadbu; a oni nechtěli přijíti.
Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
4 Opět poslal jiné služebníky, řka: Povězte pozvaným: Aj, oběd můj připravil jsem, volové moji a krmný dobytek zbit jest, a všecko hotovo. Pojďtež na svadbu.
Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
5 Ale oni nedbavše na to, odešli, jiný do vsi své a jiný po kupectví svém.
Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
6 Jiní pak zjímavše služebníky jeho a posměch jim učinivše, zmordovali.
Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
7 A uslyšav to král, rozhněval se; a poslav vojska svá, zhubil vražedníky ty a město jejich zapálil.
Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8 Tedy řekl služebníkům svým: Svadba zajisté hotova jest, ale ti, kteříž pozváni byli, nebyli hodni.
Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
9 Protož jděte na rozcestí, a kteréžkoli naleznete, zovtež na svadbu.
Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
10 I vyšedše služebníci ti na cesty, shromáždili všecky, kteréžkoli nalezli, zlé i dobré. A naplněna jest svadba hodovníky.
Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11 Tedy všed král, aby pohleděl na hodovníky, uzřel tam člověka neoděného rouchem svadebním.
Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
12 I řekl jemu: Příteli, kteraks ty sem všel, nemaje roucha svadebního? A on oněměl.
Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13 Tedy řekl král služebníkům: Svížíce ruce jeho i nohy, vezměte ho, a uvrztež jej do temností zevnitřních. Tamť bude pláč a škřipení zubů.
Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
14 Nebo mnoho jest povolaných, ale málo vyvolených.
Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
15 Tedy odšedše farizeové, radili se, jak by polapili jej v řeči.
Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
16 I poslali k němu učedlníky své s herodiány, řkouce: Mistře, víme, že pravdomluvný jsi a cestě Boží v pravdě učíš a nedbáš na žádného; nebo nepatříš na osobu lidskou.
Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
17 Protož pověz nám, co se tobě zdá: Sluší-li daň dáti císaři, čili nic?
To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
18 Znaje pak Ježíš zlost jejich, řekl: Co mne pokoušíte, pokrytci?
Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
19 Ukažte mi peníz daně. A oni podali mu peníze.
Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
20 I řekl jim: Èí jest tento obraz a svrchu napsání?
Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
21 Řekli mu: Císařův. Tedy dí jim: Dejtež, co jest císařova, císaři, a co jest Božího, Bohu.
Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
22 To uslyšavše, divili se, a opustivše jej, odešli.
Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23 V ten den přišli k němu saduceové, kteříž praví, že není z mrtvých vstání. I otázali se ho,
A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
24 Řkouce: Mistře, Mojžíš pověděl: Umřel-li by kdo, nemaje dětí, aby bratr jeho právem švagrovství pojal ženu jeho a vzbudil símě bratru svému.
cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25 I bylo u nás sedm bratrů. První pojav ženu, umřel, a nemaje semene, zůstavil ženu svou bratru svému.
Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
26 Takž podobně i druhý, i třetí, až do sedmého.
Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
27 Nejposléze pak po všech umřela i žena.
Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
28 Protož při vzkříšení kterého z těch sedmi bude žena? Nebo všickni ji měli.
To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
29 I odpověděv Ježíš, řekl jim: Bloudíte, neznajíce Písem ani moci Boží.
Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
30 Však při vzkříšení ani se nebudou ženiti ani vdávati, ale budou jako andělé Boží v nebi.
Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31 O vzkříšení pak mrtvých zdaliž jste nečtli, co jest vám povědíno od Boha, kterýž takto dí:
Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
32 Já jsem Bůh Abrahamův a Bůh Izákův a Bůh Jákobův; a Bůhť není Bůh mrtvých, ale živých.
'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
33 A slyševše to zástupové, divili se učení jeho.
Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 Farizeové pak uslyšavše, že by k mlčení přivedl saducejské, sešli se v jedno.
Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
35 I otázal se ho jeden z nich zákoník nějaký, pokoušeje ho, a řka:
Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
36 Mistře, které jest přikázání veliké v Zákoně?
“Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
37 I řekl mu Ježíš: Milovati budeš Pána Boha svého z celého srdce svého a ze vší duše své a ze vší mysli své.
Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
38 To jest přední a veliké přikázání.
Wannan itace babbar doka ta farko.
39 Druhé pak jest podobné tomu: Milovati budeš bližního svého jako sebe samého.
Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
40 Na těch dvou přikázáních všecken Zákon záleží i Proroci.
Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
41 A když se sešli farizeové, otázal se jich Ježíš,
Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
42 Řka: Co se vám zdá o Kristu? Èí jest syn? Řkou jemu: Davidův.
Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
43 Dí jim: Kterakž pak David v Duchu nazývá ho Pánem, řka:
Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
44 Řekl Pán Pánu mému: Seď na pravici mé, dokavadž nepodložím nepřátel tvých, aby byli za podnože noh tvých?
“Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
45 Poněvadž tedy David Pánem ho nazývá, i kterakž syn jeho jest?
Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
46 A nižádný nemohl jemu odpovědíti slova, aniž se odvážil kdo více od toho dne jeho se nač tázati.
Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.