< Matouš 2 >
1 Když se pak narodil Ježíš v Betlémě Judově, za dnů Herodesa krále, aj, mudrci od východu slunce přijeli do Jeruzaléma,
Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
2 Řkouce: Kde jest ten, kterýž se narodil Král Židovský? Nebo viděli jsme hvězdu jeho na východu slunce, a přijeli jsme klaněti se jemu.
suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
3 To uslyšev Herodes král, zarmoutil se i všecken Jeruzalém s ním.
Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
4 A svolav všecky přední kněží a učitele lidu, tázal se jich, kde by se Kristus měl naroditi.
Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
5 Oni pak řekli jemu: V Betlémě Judově. Nebo tak jest psáno skrze proroka:
Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
6 A ty Betléme, země Judská, nikoli nejsi nejmenší mezi knížaty Judskými; neboť z tebe vyjde Vývoda, kterýž pásti bude lid můj Izraelský.
“‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
7 Tedy Herodes tajně povolav mudrců, pilně se jich ptal, kterého by se jim času hvězda ukázala.
Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
8 A když je propouštěl do Betléma, řekl: Jdouce, ptejte se pilně na to dítě, a když naleznete, zvěstujtež mi, ať i já přijda, pokloním se jemu.
Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
9 Oni pak vyslyševše krále, jeli. A aj, hvězda, kterouž byli viděli na východu slunce, předcházela je, až i přišedši, stála nad domem, kdež bylo dítě.
Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
10 A uzřevše hvězdu, zradovali se radostí velmi velikou.
Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
11 I všedše do domu, nalezli dítě s Marijí matkou jeho, a padše, klaněli se jemu; a otevřevše poklady své, obětovali jemu dary, zlato a kadidlo a mirru.
Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
12 A od Boha napomenuti jsouce ve snách, aby se nenavraceli k Herodesovi, jinou cestou navrátili se do krajiny své.
Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
13 Když pak oni odjeli, aj, anděl Páně ukázal se Jozefovi ve snách, řka: Vstana, vezmi dítě i matku jeho, a utec do Egypta, a buď tam, dokavadž nepovím tobě; neboť bude Herodes hledati dítě, aby je zahubil.
Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
14 Kterýžto vstav hned v noci, vzal dítě i matku jeho, a odšel do Egypta.
Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
15 A byl tam až do smrti Herodesovy, aby se naplnilo povědění Páně skrze proroka, řkoucího: Z Egypta povolal jsem Syna svého.
inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
16 Tehdy Herodes uzřev, že by oklamán byl od mudrců, rozhněval se náramně, a poslav služebníky své, zmordoval všecky dítky, kteréž byly v Betlémě i ve všech končinách jeho, od dvouletých a níže, podle času, na kterýž se byl pilně vyptal od mudrců.
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17 Tehdy naplněno jest to povědění Jeremiáše proroka, řkoucího:
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18 Hlas v Ráma slyšán jest, naříkání a pláč a kvílení mnohé; Ráchel plačící synů svých, a nedala se potěšiti, protože jich není.
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
19 Když pak umřel Herodes, aj, anděl Páně ukázal se Jozefovi ve snách v Egyptě,
Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
20 Řka: Vstana, vezmi dítě i matku jeho, a jdiž do země Izraelské; neboť jsou zemřeli ti, jenž hledali bezživotí dítěte.
ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
21 Kterýžto vstav, vzal dítě i matku jeho, a přišel do země Izraelské.
Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
22 A uslyšev, že by Archelaus kraloval v Judstvu místo Herodesa otce svého, obával se tam jíti; a napomenut jsa od Boha ve snách, obrátil se do krajin Galilejských.
Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
23 A přišed, bydlil v městě, jenž slove Nazarét, aby se naplnilo, což povědíno bylo skrze proroky, že Nazaretský slouti bude.
ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”