< 3 Mojžišova 10 >
1 Synové pak Aronovi Nádab a Abiu, vzavše jeden každý kadidlnici svou, dali do nich oheň a položili na něj kadidlo, a obětovali před Hospodinem oheň cizí, čehož jim byl nepřikázal.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 Protož sstoupiv oheň od Hospodina, spálil je; a zemřeli tu před Hospodinem.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 I řekl Mojžíš Aronovi: Toť jest, což mluvil Hospodin, řka: V těch, kteříž přistupují ke mně, posvěcen budu, a před oblíčejem všeho lidu oslaven budu. I mlčel Aron.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Tedy povolal Mojžíš Mizaele a Elizafana, synů Uziele, strýce Aronova, a řekl jim: Poďte a vyneste bratří své od svatyně ven za stany.
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 I přišli a vynesli je v sukních jejich ven za stany, jakž byl rozkázal Mojžíš.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 Mluvil pak Mojžíš Aronovi, Eleazarovi a Itamarovi, synům jeho: Hlav svých neodkrývejte a roucha svého neroztrhujte, abyste nezemřeli, a aby se Bůh na všecko množství nerozhněval; ale bratří vaši, všecka rodina Izraelská, budou plakati nad tím spálením, kteréž uvedl Hospodin.
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 Vy pak ze dveří stánku úmluvy nevycházejte, abyste nezemřeli; nebo olej pomazání Hospodinova jest na vás. I učinili vedlé rozkázaní Mojžíšova.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 Mluvil také Hospodin Aronovi, řka:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 Vína a nápoje opojného nebudeš píti, ty ani synové tvoji s tebou, kdyžkoli budete míti vcházeti do stánku úmluvy, abyste nezemřeli, (ustanovení věčné to bude po rodech vašich);
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 Také abyste rozeznati mohli mezi svatým a neposvěceným, a mezi čistým a nečistým;
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 Též abyste učili syny Izraelské všechněm ustanovením, kteráž mluvil Hospodin k nim skrze Mojžíše.
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 Mluvil pak Mojžíš Aronovi, Eleazarovi a Itamarovi, synům jeho, kteříž živi zůstali: Vezměte obět suchou, kteráž zůstala z ohnivých obětí Hospodinových, a jezte ji s přesnicemi u oltáře; nebo svatá svatých jest.
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 Protož jísti budete ji na místě svatém, nebo to jest právo tvé a právo synů tvých z ohnivých obětí Hospodinových; tak zajisté jest mi přikázáno.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 Hrudí pak sem i tam obracení, a plece vznášení jísti budete na místě čistém, ty i synové tvoji, i dcery tvé s tebou; nebo to právem tobě a synům tvým dáno jest z pokojných obětí synů Izraelských.
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Plece vzhůru vznášení a hrudí sem i tam obracení s obětmi ohnivými tuků, kteréž přinesou, aby sem i tam obracíno bylo, tak jako obět obracení před Hospodinem, bude tobě i synům tvým s tebou právem věčným, jakož přikázal Hospodin.
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Mojžíš pak hledal pilně kozla k oběti za hřích, a hle, již spálen byl. Tedy rozhněval se na Eleazara a Itamara, syny Aronovy pozůstalé, a řekl:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 Pročež jste nejedli oběti za hřích na místě svatém? Nebo svatá svatých byla, poněvadž ji dal vám, abyste nesli nepravost všeho množství k očištění jejich před Hospodinem.
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 A hle, ani krev její není vnesena do vnitřku svatyně. Jísti jste měli ji v svatyni, jakož jsem byl přikázal.
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Tedy odpověděl Aron Mojžíšovi: Aj, dnes obětovali obět svou za hřích a obět svou zápalnou před Hospodinem, ale přihodila se mně taková věc, že, kdybych byl jedl obět za hřích dnes, zdali by se to líbilo Hospodinu?
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 Což když uslyšel Mojžíš, přestal na tom.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.