< Plaè 3 >

1 Já jsem muž okoušející trápení od metly rozhněvání Božího.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Zahnal mne, a uvedl do tmy a ne k světlu.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Toliko proti mně se postavuje, a obrací ruku svou přes celý den.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Uvedl sešlost na tělo mé a kůži mou, a polámal kosti mé.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Zastavěl mne a obklíčil přeodpornou hořkostí.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Postavil mne v tmavých místech jako ty, kteříž již dávno zemřeli.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Ohradil mne, abych nevyšel; obtížil ocelivý řetěz můj.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 A jakžkoli volám a křičím, zacpává uši před mou modlitbou.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Ohradil cesty mé tesaným kamenem, a stezky mé zmátl.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Jest nedvěd číhající na mne, lev v skrejších.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Cesty mé stočil, anobrž roztrhal mne, a na to mne přivedl, abych byl pustý.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Natáhl lučiště své, a vystavil mne za cíl střelám.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Postřelil ledví má střelami toulu svého.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Jsem v posměchu se vším lidem svým, a písničkou jejich přes celý den.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Sytí mne hořkostmi, opojuje mne pelynkem.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Nadto potřel o kameníčko zuby mé, vrazil mne do popela.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Tak jsi vzdálil, ó Bože, duši mou od pokoje, až zapomínám na pohodlí,
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 A říkám: Zahynulatě síla má i naděje má, kterouž jsem měl v Hospodinu.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 A však duše má rozvažujíc trápení svá a pláč svůj, pelynek a žluč,
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Rozvažujíc to ustavičně, ponižuje se ve mně.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 A přivodě sobě to ku paměti, (naději mám),
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Že veliké jest milosrdenství Hospodinovo, když jsme do konce nevyhynuli. Nepřestávajíť zajisté slitování jeho,
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Ale nová jsou každého jitra; převeliká jest pravda tvá.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Díl můj jest Hospodin, říká duše má; protož naději mám v něm.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Dobrý jest Hospodin těm, jenž očekávají na něj, duši té, kteráž ho hledá.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Dobré jest trpělivě očekávajícímu na spasení Hospodinovo.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Dobré jest muži tomu, kterýž by nosil jho od dětinství svého,
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Kterýž by pak byl opuštěn, trpělivě se má v tom, což na něj vloženo,
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Dávaje do prachu ústa svá, až by se ukázala naděje,
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Nastavuje líce tomu, kdož jej bije, a sytě se potupou.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Neboť nezamítá Pán na věčnost;
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Nýbrž ačkoli zarmucuje, však slitovává se podlé množství milosrdenství svého.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Netrápíť zajisté z srdce svého, aniž zarmucuje synů lidských.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Aby kdo potíral nohama svýma všecky vězně v zemi,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Aby nespravedlivě soudil muže před oblíčejem Nejvyššího,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Aby převracel člověka v při jeho, Pán nelibuje.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Kdo jest, ješto když řekl, stalo se něco, a Pán nepřikázal?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Z úst Nejvyššího zdali nepochází zlé i dobré?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Proč by tedy sobě stýskal člověk živý, muž nad kázní za hříchy své?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Zpytujme raději a ohledujme cest našich, a navraťme se až k Hospodinu.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Pozdvihujme srdcí i rukou svých k Bohu silnému v nebe.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Myť jsme se zpronevěřili, a zpurní jsme byli, protož ty neodpouštíš.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Obestřels se hněvem a stiháš nás, morduješ a nešanuješ.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Obestřels se oblakem, aby nemohla proniknouti k tobě modlitba.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Za smeti a povrhel položil jsi nás u prostřed národů těchto.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Rozdírají na nás ústa svá všickni nepřátelé naši.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Strach a jáma potkala nás, zpuštění a setření.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Potokové vod tekou z očí mých pro potření dcery lidu mého.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Oči mé slzí bez přestání, proto že není žádného odtušení,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Ažby popatřil a shlédl Hospodin s nebe.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Oči mé rmoutí duši mou pro všecky dcery města mého.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Loviliť jsou mne ustavičně, jako ptáče, nepřátelé moji bez příčiny.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Uvrhli do jámy život můj, a přimetali mne kamením.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Rozvodnily se vody nad hlavou mou, řekl jsem: Jižtě po mně.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Vzývám jméno tvé, ó Hospodine, z jámy nejhlubší.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Hlas můj vyslýchával jsi; nezacpávejž ucha svého před vzdycháním mým a voláním mým.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 V ten den, v němž jsem tě vzýval, přicházeje, říkávals: Neboj se.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Pane, zasazuje se o při duše mé, vysvobozoval jsi život můj.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Vidíš, ó Hospodine, převrácenost, kteráž se mně děje, dopomoziž mi k spravedlnosti.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Vidíš všecko vymstívání se jejich, všecky úklady jejich proti mně.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Slýcháš utrhání jejich, ó Hospodine, i všecky obmysly jejich proti mně,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 Řeči povstávajících proti mně, a přemyšlování jejich proti mně přes celý den.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Pohleď, jak při sedání jejich i povstání jejich jsem písničkou jejich.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Dej jim odplatu, Hospodine, podlé díla rukou jejich.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Dej jim zatvrdilé srdce a prokletí své na ně.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Stihej v prchlivosti, a vyhlaď je, ať nejsou pod nebem tvým.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Plaè 3 >