< Sudcov 16 >

1 Odšel pak Samson do Gázy, a uzřev tam ženu nevěstku, všel k ní.
Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
2 I povědíno obyvatelům Gázy: Samson přišel sem. Kteříž obeslavše se, střáhli na něj v bráně města přes celou noc, a stavěli se tiše té celé noci, řkouce: Až ráno zabijeme jej.
Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
3 Spal pak Samson až do půl noci, a o půl noci vstal, a pochytiv vrata brány městské s oběma veřejemi a s závorou, vložil na ramena svá a vnesl je na vrch hory, kteráž byla naproti Hebronu.
Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
4 Potom pak zamiloval ženu v údolí Sorek, jejíž jméno bylo Dalila.
Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
5 I přišli knížata Filistinská k ní a řekli jí: Oklamej ho a zvěz, v čem jest síla jeho tak veliká, a jak bychom přemohli jej, abychom svížíce, skrotili jej; tobě pak jeden každý z nás dáme tisíc a sto lotů stříbra.
Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
6 Tedy řekla Dalila Samsonovi: Prosím, oznam mi, v čem jest tak veliká síla tvá, a čím bys svázán a zemdlen býti mohl?
Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
7 Odpověděl jí Samson: Kdyby mne svázali sedmi houžvemi surovými, kteréž ještě neuschly, tedy zemdlím, a budu jako jiný člověk.
Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
8 I přinesli jí knížata Filistinská sedm houžví surových, kteréž ještě neuschly, a svázala ho jimi.
Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
9 (V zálohách pak nastrojeni byli někteří u ní v komoře.) I řekla jemu: Filistinští na tě, Samsone. A on roztrhl houžve, jako by přetrhl nit koudelnou, přistrče k ohni, a není poznána síla jeho.
Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
10 Tedy řekla Dalila Samsonovi: Aj, oklamals mne a lživě jsi mi mluvil. Prosím, oznam mi nyní, čím bys mohl svázán býti?
Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
11 Kterýž odpověděl jí: Kdyby mne tuze svázali novými provazy, jimiž by ještě nic děláno nebylo, tedy zemdlím a budu jako kdokoli jiný z lidí.
Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
12 I vzala Dalila provazy nové a svázala ho jimi, a řekla jemu: Filistinští na tě, Samsone. (Zálohy pak nastrojeny byly v komoře.) I roztrhl je na rukou svých jako nitku.
Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
13 Tedy řekla Dalila Samsonovi: Až dosavad jsi mne svodil, a mluvils mi lež. Pověziž mi, čím bys svázán býti mohl. Odpověděl jí: Kdybys přivila sedm pramenů z vlasů hlavy mé k vratidlu tkadlcovskému.
Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
14 Což učinivši, zarazila hřebem, a řekla jemu: Filistinští na tě, Samsone. A procítiv ze sna svého, vytrhl hřeb, osnovu i s vratidlem.
ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
15 Opět řekla jemu: Kterak ty pravíš: Miluji tě, poněvadž srdce tvé není se mnou? Již jsi mne potřikrát oklamal a neoznámils mi, v čem jest tak veliká síla tvá.
Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
16 Když tedy trápila jej slovy svými každého dne, a obtěžovala jej, umdlena jest duše jeho, jako by již měl umříti.
Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
17 I otevřel jí cele srdce své a řekl jí: Břitva nevešla nikdy na hlavu mou, nebo Nazarejský Boží jsem od života matky své. Kdybych oholen byl, odešla by ode mne síla má, a zemdlel bych a byl jako jiný člověk.
Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
18 Viduci pak Dalila, že by cele otevřel jí srdce své, poslala a zavolala knížat Filistinských těmi slovy: Poďte ještě jednou, nebo otevřel mi cele srdce své. Tedy přišli knížata Filistinská k ní, nesouce stříbro v rukou svých.
Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
19 I uspala ho na klíně svém a povolala holiče, i dala oholiti sedm pramenů vlasů hlavy jeho. I počala jím strkati, když odešla od něho síla jeho.
Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
20 A řekla: Filistinští na tě, Samsone. Procítiv pak ze sna svého, řekl: Vyjdu jako i prvé, a probiji se skrze ně. Nevěděl však, že Hospodin odstoupil od něho.
Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
21 Tedy javše ho Filistinští, vyloupili mu oči, a dovedše ho do Gázy, svázali jej dvěma řetězy železnými. A mlel v domě vězňů.
Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
22 Potom počaly mu vlasy na hlavě odrostati po oholení.
Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
23 Knížata pak Filistinská shromáždili se, aby obětovali obět velikou bohu svému Dágonovi a aby se veselili; nebo řekli: Dalť jest bůh náš v ruce naše Samsona nepřítele našeho.
To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
24 A když uzřel jej lid, chválili boha svého; nebo pravili: Dalť jest bůh náš v ruce naše nepřítele našeho a zhoubce země naší, kterýž mnohé z našich zmordoval.
Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
25 I stalo, když se rozveselilo srdce jejich, že řekli: Zavolejte Samsona, aby kratochvílil před námi. Tedy povolali Samsona z domu vězňů, aby hral před nimi; i postavili ho mezi sloupy.
Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
26 Nebo řekl Samson pacholeti, kteréž ho za ruku vodilo: Přiveď mne, ať mohu omakati sloupy, na nichž dům stojí, a zpodepříti se na ně.
sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
27 Dům pak plný byl mužů a žen, a byla tam všecka knížata Filistinská, ano i na vrchu okolo tří tisíc mužů a žen, kteříž dívali se, když Samson hral.
To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
28 I volal Samson k Hospodinu, a řekl: Panovníče Hospodine, prosím, rozpomeň se na mne, a posilni mne, žádám, toliko aspoň jednou, ó Bože, abych se jednou pomstíti mohl za své obě oči nad Filistinskými.
Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
29 Objav tedy Samson oba sloupy prostřední, na nichž dům ten stál, zpolehl na ně, na jeden pravou a na druhý levou rukou svou.
Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
30 Potom řekl Samson: Nechť umře život můj s Filistinskými. A nalehl silně, i padl dům na knížata a na všecken lid, kterýž byl v něm; i bylo mrtvých, kteréž pobil on umíraje, více než těch, kteréž pobil, živ jsa.
Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
31 Tedy přišli přátelé jeho, a všecken dům otce jeho, a vzavše jej, odešli, a pochovali jej mezi Zaraha a Estaol v hrobě Manue otce jeho. A on soudil lid Izraelský dvadceti let.
Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.

< Sudcov 16 >