< Józua 9 >
1 To když uslyšeli všickni králové, kteříž bydlili za Jordánem, na horách i na rovinách, a na všem břehu moře velikého naproti Libánu: Hetejský, Amorejský, Kananejský, Ferezejský, Hevejský a Jebuzejský,
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 Sebrali se spolu, aby bojovali proti Jozue a proti Izraeli jednomyslně.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 Ale obyvatelé Gabaon uslyšavše, co učinil Jozue Jerichu a Hai,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 Učinili i oni chytře. Nebo odšedše, ukázali se, jako by zdaleka poslové byli, a vzali pytle staré na osly své, a kožené láhvice vinné vetché, zedrané a zzašívané,
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 Obuv také starou a splácenou na nohy své, též šaty otřelé na sebe; a všecken chléb, kterýž sobě na cestu vzali, vyschlý byl a zdrobený.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 I šli k Jozue do ležení v Galgala, a řekli jemu i mužům Izraelským: Z země daleké jsme přišli, protož nyní učiňte s námi smlouvu.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 Tedy odpověděli muži Izraelští k Hevejským: Snad u prostřed nás vy bydlíte, i kterakž bychom s vámi učinili smlouvu?
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 Ale oni odpověděli Jozue: Služebníci tvoji jsme. Jimž řekl Jozue: Kdo pak jste, a odkud jste přišli?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 Odpověděli jemu: Z země velmi daleké přišli služebníci tvoji ve jménu Hospodina Boha tvého; nebo jsme slyšeli pověst jeho a všecky věci, kteréž činil v Egyptě.
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 A všecko, což učinil dvěma králům Amorejským, kteříž bydlili za Jordánem, Seonovi, králi Ezebon, a Ogovi, králi Bázan, kterýž byl v Astarot.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 I řekli nám starší naši a všickni obyvatelé země naší těmito slovy: Nabeřte sobě potravy na cestu, a jděte jim vstříc, a rcete jim: Služebníci vaši jsme, protož nyní učiňte s námi smlouvu.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 Totoť jest chléb náš; horký jsme na cestu vzali z domů svých v ten den, když jsme vyšli, abychom k vám šli, a hle, nyní již vyschl a zdrobil se.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 A tyto kožené láhvice vinné nové byly, když jsme je naplnili, a již hle, potrhané jsou; tolikéž tento oděv náš a obuv naše zvetšela, pro přílišnou cesty dalekost.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 I přijali to muži ti z pokrmů jejich, a úst Hospodinových neotázali se.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 A učinil s nimi Jozue pokoj, a všel s nimi v smlouvu, aby jich při životu zanechal; také i knížata shromáždění přísahu jim učinili.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Po třech pak dnech, po té smlouvě s nimi učiněné, uslyšeli, že by velmi blízko jich byli, a že by u prostřed nich bydlili.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 Jdouce tedy synové Izraelští, přitáhli k městům jejich třetího dne; města pak jejich byla Gabaon a Kafira a Berot a Kariatjeharim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Ale nezbili jich synové Izraelští, proto že přísahu jim učinili knížata shromáždění skrze Hospodina Boha Izraelského. A reptalo všecko shromáždění proti knížatům.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Tedy řekla všecka knížata všemu shromáždění: My jsme jim přísahu učinili skrze Hospodina Boha Izraelského, protož nyní nemůžeme se jich dotknouti.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 Toto jim učiníme: Zanecháme jich při životu, aby nebylo na nás rozhněvání pro přísahu, kterouž jsme jim učinili.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 Řekli jim knížata i to: Nechť jsou živi a drva sekají, a vodu nosí všemu shromáždění. I přestali na tom, jakož jim mluvila knížata.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Povolal jich pak Jozue a mluvil k nim, řka: Proč jste nás podvedli, řkouce: Velmi jsme dalecí od vás? A vy u prostřed nás bydlíte.
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Protož nyní zlořečení jste, a nepřestanou z vás služebníci, a kteříž by dříví sekali a vodu nosili do domu Boha mého.
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Kteříž odpovídajíce Jozue, řekli: Za věc jistou oznámeno bylo služebníkům tvým, kterak přikázal Hospodin Bůh tvůj Mojžíšovi služebníku svému, dáti vám zemi tuto, a vyhladiti všecky obyvatele země této před tváří vaší; protož strachovali jsme se vás, bojíce se za životy své před vámi, a učinili jsme to.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 A hle, nyní v ruce tvé jsme; cožť se dobrého a spravedlivého vidí učiniti s námi, to učiň.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 I učinil jim tak, a vysvobodil je z rukou synů Izraelských, aby jich nepobili.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 A ustanovil je Jozue v ten den, aby dříví sekali a vodu nosili všemu shromáždění, i k oltáři Hospodinovu, až do tohoto dne, na místě, kteréž by vyvolil.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.