< Jan 1 >

1 Na počátku bylo Slovo, a to Slovo bylo u Boha, a to Slovo byl Bůh.
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 To bylo na počátku u Boha.
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 Všecky věci skrze ně učiněny jsou, a bez něho nic není učiněno, což učiněno jest.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 V něm život byl, a život byl světlo lidí.
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 A to Světlo v temnostech svítí, ale tmy ho neobsáhly.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Byl člověk poslaný od Boha, jemuž jméno bylo Jan.
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Ten přišel na svědectví, aby svědčil o tom Světle, aby všickni uvěřili skrze něho.
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 Nebyl on to Světlo, ale poslán byl, aby svědectví vydával o tom Světle.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 Tenť byl to pravé Světlo, jenž osvěcuje každého člověka přicházejícího na svět.
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 Na světě byl, a svět skrze něho učiněn jest, a svět ho nepoznal.
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 Do svého vlastního přišel, a vlastní jeho nepřijali ho.
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 Kteříž pak koli přijali jej, dal jim moc syny Božími býti, totiž těm, kteříž věří ve jméno jeho,
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 Kteřížto ne ze krví, ani z vůle těla, ani z vůle muže, ale z Boha zplozeni jsou.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 A Slovo to tělo učiněno jest, a přebývalo mezi námi, (a viděli jsme slávu jeho, slávu jakožto jednorozeného od Otce, ) plné milosti a pravdy.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 Jan svědectví vydával o něm, a volal, řka: Tentoť jest, o němž jsem pravil, že po mně přišed, předšel mne; nebo přednější jest nežli já.
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 A z plnosti jeho my všickni vzali jsme, a to milost za milost.
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 Nebo zákon skrze Mojžíše dán jest, ale milost a pravda skrze Ježíše Krista stala se jest.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 Boha žádný nikdy neviděl, ale jednorozený Syn, kterýž jest v lůnu Otce, onť jest nám vypravil.
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 A totoť jest svědectví Janovo, když poslali Židé z Jeruzaléma kněží a Levíty, aby se ho otázali: Ty kdo jsi?
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 I vyznal a nezapřel, a vyznal: Že já nejsem ten Kristus.
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 I otázali se ho: Což pak? Eliáš jsi ty? I řekl: Nejsem. Tedy jsi ten Prorok? Odpověděl: Nejsem.
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 I řekli jemu: Kdožs pak? Ať odpověd dáme těm, kteříž nás poslali. Co pravíš sám o sobě?
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 Řekl: Já jsem hlas volajícího na poušti: Spravte cestu Páně, jakož pověděl Izaiáš prorok.
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 Ti pak, kteříž byli posláni, z farizeů byli.
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 I otázali se ho a řekli jemu: Pročež tedy křtíš, poněvadž ty nejsi Kristus, ani Eliáš, ani Prorok?
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 Odpověděl jim Jan, řka: Já křtím vodou, ale uprostřed vás stojí, jehož vy neznáte.
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 Ten ačkoli po mně přišel, však předšel mne, u jehožto obuvi já nejsem hoden rozvázati řeménka.
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 Toto v Betabaře stalo se za Jordánem, kdežto Jan křtil.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 Druhého pak dne uzřel Jan Ježíše, an jde k němu. I dí: Aj, Beránek Boží, kterýž snímá hřích světa.
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 Tentoť jest, o kterémž jsem já pravil, že za mnou jde muž, kterýž mne předšel; nebo přednější jest nežli já.
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 A já jsem ho neznal, ale aby zjeven byl lidu Izraelskému, proto jsem já přišel, křtě vodou.
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 A svědectví vydal Jan, řka: Viděl sem Ducha sstupujícího jako holubice s nebe, a zůstal na něm.
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 A já jsem ho neznal, ale kterýž mne poslal křtíti vodou, ten mi řekl: Nad kýmž uzříš Ducha sstupujícího a zůstávajícího na něm, tenť jest, kterýž křtí Duchem svatým.
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 A já jsem viděl, a svědectví jsem vydal, že on jest ten Syn Boží.
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 Druhého pak dne opět stál Jan, a z učedlníků jeho dva,
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 A uzřev Ježíše, an se prochází, řekl: Aj, Beránek Boží.
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 I slyšeli ho dva učedlníci mluvícího, a šli za Ježíšem.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 I obrátiv se Ježíš, a uzřev je, ani jdou za ním, dí jim: Co hledáte? A oni řekli jemu: Rabbi, (jenž se vykládá: Mistře, ) kde bydlíš?
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 Dí jim: Pojďte a vizte. I šli, aby viděli, kde by bydlil, a zůstali u něho ten den; neb bylo již okolo desáté hodiny.
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 Byl pak Ondřej, bratr Šimona Petra, jeden ze dvou, kteříž byli to slyšeli od Jana, a šli za ním.
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 I nalezl ten první bratra svého vlastního Šimona, a řekl mu: Nalezli jsme Mesiáše, jenž se vykládá Kristus.
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 I přivedl jej k Ježíšovi. A pohleděv naň Ježíš, dí: Ty jsi Šimon, syn Jonášův, ty slouti budeš Céfas, jenž se vykládá Petr.
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 Na druhý pak den Ježíš chtěl vyjíti do Galilee, i nalezl Filipa, a řekl jemu: Pojď za mnou.
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 A byl Filip z Betsaidy, města Ondřejova a Petrova.
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Nalezl také Filip Natanaele. I dí jemu: O kterémž psal Mojžíš v Zákoně a Proroci, nalezli jsme Ježíše, syna Jozefova z Nazaréta.
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 I řekl jemu Natanael: A může z Nazaréta co dobrého býti? Řekl jemu Filip: Pojď a viz.
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 Vida Ježíš Natanaele, an jde k němu, i dí o něm: Aj, právě Izraelitský, v němžto lsti není.
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Řekl mu Natanael: Jakž ty mne znáš? Odpověděl Ježíš a řekl jemu: Prve nežli tě Filip zavolal, kdyžs byl pod fíkem, viděl jsem tebe.
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Odpověděl Natanael a řekl jemu: Mistře, ty jsi Syn Boží, ty jsi ten Král Izraelský.
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Odpověděl Ježíš a řekl jemu: Žeť jsem řekl: Viděl jsem tebe pod fíkem, věříš? Větší věci nad tyto uzříš.
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 I dí mu: Amen, amen pravím vám: Od tohoto času uzříte nebe otevřené, a anděly Boží vstupující a sstupující na Syna člověka.
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< Jan 1 >