< Jeremiáš 5 >

1 Zběhejte ulice Jeruzalémské, pohleďte nyní, a zvězte, a hledejte v ulicích jeho, naleznete-li muže, jest-li kdo, ješto by činil soud, a vyhledával toho, což pravého jest, a odpustím jemu.
“Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
2 Ale i když říkají: Živť jest Hospodin, takovým způsobem křivě přisahají.
Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
3 Ó Hospodine, zdaliž oči tvé nepatří na pravdu? Biješ je, ale necítí bolesti; hubíš je, ale nechtí přijímati kázně. Tvrdší jsou tváře jejich než skála, nechtí se navrátiti.
Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
4 I řekl jsem já: Snad tito prostí jsou, nerozumně sobě počínají; nebo nejsou povědomi cesty Hospodinovy, soudu Boha svého.
Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
5 Půjdu aspoň k přednějším, a mluviti budu k nim; nebo oni povědomi jsou cesty Hospodinovy, soudu Boha svého. Ale i ti spolu polámali jho, roztrhali svazky.
Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
6 Protož je podáví lev z lesa, vlk večerní pohubí je, pardus číhati bude u měst jejich. Kdožkoli vyjde z nich, roztrhán bude; nebo mnohá jsou přestoupení jejich, rozmohly se převrácenosti jejich.
Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
7 Kdež jest to, pročež bych měl odpustiti tobě? Synové tvoji opouštějí mne, a přisahají skrze ty, kteříž nejsou bohové. Jakž jsem jen nasytil je, hned cizoloží, a do domu nevěstky houfem se valí.
“Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
8 Ráno vstávajíce, jsou jako koni vytylí; každý k ženě bližního svého řehce.
An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
9 Zdaliž pro takové věci nemám navštíviti? dí Hospodin. A zdali nad národem takovým nemá mstíti duše má?
Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
10 Vstupte na zdi jeho, a zkazte je, a nepřestávejte; svrzte štítky zdí jeho, nebo nejsou Hospodinovy.
“Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
11 Velice zajisté zpronevěřili se mi dům Izraelský a dům Judský, dí Hospodin.
Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
12 Sčítali klam na Hospodina, a říkali: Není tak, nikoli nepřijde na nás zlé, a meče ani hladu nepocítíme.
Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
13 Ti pak proroci pominou s větrem, a žádného slova není v nich. Takť se stane jim.
Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
14 Protož takto praví Hospodin Bůh zástupů: Proto že tak mluvíte, aj, já způsobím, aby slova tvá v ústech tvých byla jako oheň, a lid tento dřívím, kteréž on zžíře.
Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
15 Aj, já přivedu na vás národ zdaleka, ó dome Izraelský, dí Hospodin, národ silný, národ starodávní, národ, jehož jazyka nebudeš uměti, ani rozuměti, co mluví.
Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
16 Jehož toul jako hrob otevřený, všickni jsou silní.
Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
17 A vytráví obilé tvé a chléb tvůj, požerou syny tvé a dcery tvé, pojí bravy tvé i skot tvůj, pojí vinné kmeny tvé i fíkoví tvé, města tvá hrazená, v nichž ty doufáš, znuzí mečem.
Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
18 A však ani těch časů, dí Hospodin, neučiním s vámi konce.
“Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
19 Nebo stane se, když řeknete: Proč nám činí Hospodin Bůh náš všecko toto? že řekneš jim: Jakož jste opustili mne, a sloužili bohům cizozemců v zemi své, tak sloužiti budete cizozemcům v zemi ne své.
Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
20 Oznamtež to v domě Jákobově, a rozhlaste v Judstvu, řkouce:
“Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
21 Slyštež nyní toto, lide bláznivý a nesmyslný, kteříž oči mají a nevidí, kteříž uši mají a neslyší:
Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
22 Což se mne nebudete báti? dí Hospodin. Což před oblíčejem mým nebudete se třásti? Kterýž jsem položil písek za cíl moři ustanovením věčným, jehož nepřekračuje. Ačkoli zmítají se, však neodolají, ačkoli zvučí vlnobití jeho, však ho nepřecházejí.
Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
23 Ale lid tento má srdce zarputilé a zpurné, odstoupili a odešli.
Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
24 Ani neřekli v srdci svém: Bojme se již Hospodina Boha našeho, kterýž dává déšť jarní i podzimní časem svým, téhodnů nařízených ke žni ostříhá nám.
Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
25 Nepravostiť vaše překážku činí těm věcem, a hříchové vaši připravují vás o to dobré.
Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
26 Nebo nalézají se v lidu mém bezbožníci; střeže jako čižebníci, kteříž lécejí, stavějí osídla, lidi lapají.
“A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
27 Jako klece plná ptáků, tak domové jejich plní jsou lsti. Protož zrostli a zbohatli,
Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
28 Vytylí jsou, lsknou se, nadto umějí se vyhýbati bídám. Pře nesoudí, ani pře sirotka, a však šťastně se jim vede, ačkoli k spravedlnosti chudým nedopomáhají.
suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
29 Zdaliž pro takové věci nemám navštíviti jich? dí Hospodin. Zdali nad národem takovým nemá mstíti duše má?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
30 Věc užasnutí hodná a hrozná děje se v zemi této.
“Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
31 Proroci prorokují lživě, a kněží panují skrze ně, a lid můj miluje to. Èeho byste pak neučinili naposledy?
Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?

< Jeremiáš 5 >