< Jeremiáš 34 >
1 Slovo, kteréž se stalo k Jeremiášovi od Hospodina, (když Nabuchodonozor král Babylonský, a všecko vojsko jeho, i všecka království země pod moc jeho přináležející, všickni také národové bojovali proti Jeruzalému a proti všechněm městům jeho), řkoucí:
Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Takto praví Hospodin Bůh Izraelský: Jdi a rci Sedechiášovi králi Judskému, rci, pravím, jemu: Takto dí Hospodin: Aj, já dám toto město v ruku krále Babylonského, aby je vypálil ohněm.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
3 I ty neznikneš ruky jeho, ale jistotně jat a v ruku jeho vydán budeš, a oči tvé uzří oči krále Babylonského, i ústa jeho s ústy tvými mluviti budou, a do Babylona se dostaneš.
Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
4 A však slyš slovo Hospodinovo, Sedechiáši králi Judský: Takto praví Hospodin o tobě: Neumřeš od meče,
“‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
5 V pokoji umřeš. A jakož pálívali otcům tvým, králům předešlým, kteříž byli před tebou, tak páliti budou tobě, a říkajíce: Ach, pane, kvíliti budou nad tebou; nebo slovo toto já mluvil jsem, dí Hospodin.
za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
6 I mluvil Jeremiáš prorok Sedechiášovi, králi Judskému, všecka slova ta v Jeruzalémě,
Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
7 Když vojsko krále Babylonského bojovalo proti Jeruzalému a proti všechněm městům Judským ostatním, proti Lachis a proti Azeku; nebo ta byla pozůstala z měst Judských města hrazená.
yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
8 Slovo, kteréž se stalo k Jeremiášovi od Hospodina, když učinil král Sedechiáš smlouvu se vším lidem, kterýž byl v Jeruzalémě, o vyhlášení jim svobody,
Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
9 Aby propustil jeden každý služebníka svého a jeden každý děvku svou, Hebrejského neb Hebrejskou, svobodné, aby nepodroboval sobě v službu Žida, bratra svého, nižádný.
Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
10 Tedy uposlechla všecka knížata a všecken lid, kterýž byl v smlouvu všel, aby propustil jeden každý služebníka svého a jeden každý děvku svou svobodné, aby nepodroboval jich v službu více; uposlechli, pravím, a propustili.
Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
11 Potom pak rozmyslivše se, zase pobrali služebníky své a děvky své, kteréž byli propustili svobodné, a podrobili je sobě za služebníky a děvky.
Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
12 I stalo se slovo Hospodinovo k Jeremiášovi od Hospodina, řkoucí:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Takto praví Hospodin Bůh Izraelský: Já jsem učinil smlouvu s otci vašimi toho dne, když jsem je vyvedl z země Egyptské, z domu služebníků, řka:
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
14 Po vyplnění sedmi let propouštívejte jeden každý bratra svého Žida, kterýž by prodán byl tobě, a sloužilť by šest let, propusť, pravím, jej svobodného od sebe. Ale neuposlechli otcové vaši mne, aniž naklonili ucha svého.
‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
15 Vy zajisté usmyslivše sobě dnes, učinili jste to, což jest spravedlivého před očima mýma, že jste vyhlásili svobodu jeden každý bližnímu svému, učinivše smlouvu před oblíčejem mým v domě tom, kterýž nazván jest od jména mého.
Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
16 Ale zase zpáčivše se, zlehčili jste jméno mé, že jste vzali zase jeden každý služebníka svého a jeden každý děvku svou, kteréž jste byli propustili svobodné podlé žádosti jejich, a podrobili jste je, aby byli vaši služebníci a děvky.
Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
17 Protož takto praví Hospodin: Vy neuposlechli jste mne, abyste vyhlásili svobodu jeden každý bratru svému, a jeden každý bližnímu svému, aj, já vyhlašuji proti vám svobodu, dí Hospodin, meči, moru a hladu, a vydám vás ku posmýkání po všech královstvích země.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
18 Vydám zajisté ty lidi, jenž přestoupili smlouvu mou, kteříž nevykonali slov smlouvy té, kterouž učinili před oblíčejem mým, když tele rozťali na dvé, a prošli mezi díly jeho,
Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
19 Totiž knížata Judská a knížata Jeruzalémská, komorníci, a kněží, i všecken lid té země, kteříž prošli mezi díly toho telete.
Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
20 Vydám je, pravím, v ruku nepřátel jejich, a v ruku hledajících bezživotí jejich, i budou těla mrtvá jejich za pokrm ptactvu nebeskému, a šelmám zemským.
zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
21 Sedechiáše také krále Judského, i knížata jeho vydám v ruku nepřátel jejich, a v ruku hledajících bezživotí jejich, v ruku, pravím, vojska krále Babylonského, kteříž odtáhli od vás.
“Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
22 Aj, já přikáži, dí Hospodin, a přivedu je zase na město toto, aby bojovali proti němu, a vezmouce je, vypálili je ohněm; města také Judská obrátím v poušť, tak že nebude žádného obyvatele.
Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”