< Jeremiáš 10 >

1 Slyšte slovo toto, kteréž mluví k vám Hospodin, ó dome Izraelský.
Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
2 Takto praví Hospodin: Cestě pohanů neučte se, aniž se znamení nebeských děste, neboť se jich děsí pohané.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
3 Ustanovení zajisté těch národů jsou pouhá marnost. Nebo setna dřevo sekerou v lese, dílo rukou řemeslníka,
Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
4 Stříbrem a zlatem ozdobí je, hřebíky a kladivy utvrzují je, aby se neviklalo.
Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
5 Jsou jako palmový špalek tvrdý, ani nemluví; nošeni býti musejí, nebo choditi nemohou. Nebojtež se jich, nebo zle učiniti nemohou, aniž také dobře učiniti mohou.
Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
6 Z nichž není žádného tobě podobného, ó Hospodine; veliký jsi, i jméno tvé veliké jest v moci.
Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
7 Kdož by se nebál tebe, králi národů? Na tebeť zajisté to sluší, poněvadž mezi všemi mudrci národů, i ve všem království jejich nikdá nebylo podobného tobě.
Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
8 A však ze spolka zhlupěli, a blázni jsou; z dřeva učiti se jest pouhá marnost.
Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
9 Stříbro tažené z zámoří přivážíno bývá, a zlato z Ufaz, dílo řemeslníka a rukou zlatníka; z postavce modrého a šarlatový jest oděv jejich, všecko to jest dílo umělých.
An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
10 Ale Hospodin jest Bůh pravý, jest Bůh živý a král věčný, před jehož prchlivostí země se třese, aniž mohou snésti národové rozhněvání jeho.
Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
11 (Takto říkejte jim: Bohové ti, kteříž nebe ani země neučinili, nechť zahynou z země, a nechť jich není pod nebem.)
“Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
12 Kterýž učinil zemi mocí svou, kterýž utvrdil okršlek světa moudrostí svou, a opatrností svou roztáhl nebesa.
Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
13 Kterýžto když vydává hlas, ječení vod bývá na nebi, a kterýž působí to, aby vystupovaly páry od kraje země, blýskání s deštěm přivodí, a vyvodí vítr z pokladů svých.
Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
14 Tak zhlupěl každý člověk, že nezná toho, že zahanben bývá každý zlatník pro rytinu; nebo slitina jeho jest faleš, a není ducha v nich.
Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
15 Marnost jsou a dílo podvodů; v čas, v němž je navštívím, zahynou.
Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
16 Neníť podobný těmto díl Jákobův, nebo on jest stvořitel všeho; Izrael tolikéž jest pokolení dědictví toho, jehož jméno jest Hospodin zástupů.
Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
17 Sbeř z země koupi svou, ty kteráž bydlíš v pevnosti této.
Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
18 Nebo takto praví Hospodin: Aj, já vyhodím z praku obyvatele země této pojednou, a ssoužím je, aby shledali toto:
Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
19 Běda mně pro setření mé, přebolestná jest rána má, ješto jsem já byl řekl: Jistě tuto nemoc budu moci snésti.
Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
20 Stan můj popléněn jest, a všickni provazové moji potrháni jsou. Synové moji odebrali se ode mne, a není žádného; není žádného, kdo by více rozbíjel stan můj, a roztáhl kortýny mé.
An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
21 Nebo zhlupěli pastýři, a Hospodina se nedotazovali; protož nevede se jim šťastně, a všecko stádo pastvy jejich rozptýleno jest.
Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
22 Aj, pověst jistá přichází, a pohnutí veliké z země půlnoční, aby obrácena byla města Judská v pustinu a v příbytek draků.
Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
23 Vím, Hospodine, že není v moci člověka cesta jeho, aniž jest v moci muže toho, kterýž chodí, aby spravoval krok svůj.
Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
24 Kárej mne, Hospodine, však milostivě, ne v hněvě svém, abys nesetřel mne.
Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
25 Vylí hněv svůj na ty národy, kteříž tebe neznají, a na rodiny, kteréž jména tvého nevzývají; nebo zžírají Jákoba, a tak zžírají jej, aby jej všeho sežrali, a obydlí jeho v poustku obrátili.
Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.

< Jeremiáš 10 >