< Ezechiel 6 >
1 I stalo se ke mně slovo Hospodinovo, řkoucí:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Synu člověčí, obrať tvář svou proti horám Izraelským, a prorokuj proti nim,
“Ɗan mutum, ka kafa idonka a kan duwatsun Isra’ila; ka yi annabci a kansu
3 A rci: Hory Izraelské, slyšte slovo Panovníka Hospodina: Takto praví Panovník Hospodin horám a pahrbkům, prudkým potokům a údolím: Aj, já, já uvedu na vás meč, a zkazím výsosti vaše.
ka ce, ‘Ya ku duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa duwatsu da tuddai, ga rafuffuka da kuma kwaruruka. Ina shirin kawo takobi a kanku, kuma zan hallaka masujadanku.
4 A tak zpustnou oltářové vaši, a ztroskotáni budou sluneční obrazové vaši, a rozmeci zbité vaše před ukydanými bohy vašimi.
Za a ragargaza bagadanku a kuma farfasa bagadanku na ƙone turare; zan kuma kashe mutanenku a gaban gumakanku.
5 Povrhu také mrtvá těla synů Izraelských před ukydanými bohy jejich, a rozptýlím kosti vaše okolo oltářů vašich.
Zan shimfiɗa gawawwakin Isra’ilawa a gaban gumakansu, in kuma watsar da ƙasusuwanku kewaye da bagadanku.
6 Kdekoli bydliti budete, města zpuštěna budou, a výsosti zpustnou. Pročež popléněni budou a zpustnou i oltářové vaši, potroskotáni budou a přestanou ukydaní bohové vaši, a sluneční obrazové vaši zpodtínáni, a tak vyhlazena budou díla vaše.
Duk inda kuke zama, garuruwa za su zama kango, za a kuma ragargaza masujadai, saboda bagadanku su rurrushe su zama kango, a kuma farfasa gumakanku su lalace, za a rurrushe bagadan ƙone turarenku, a kuma shafe dukan abin da kuka yi.
7 I padnou zbití u prostřed vás, a zvíte, že já jsem Hospodin.
Za a kashe mutanenku a cikinku, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.
8 A pozůstavím některé z vás, kteříž by ušli meče, mezi pohany, když rozptýleni budete do zemí.
“‘Amma zan bar waɗansu, gama waɗansunku za su tsere wa takobi sa’ad da aka watsar da ku a cikin ƙasashe da al’ummai.
9 I budou se rozpomínati na mne, kteříž z vás zachováni budou mezi národy, mezi něž budou zajati, že jsem kormoucen byl srdcem jejich smilným, kteréž odstoupilo ode mne, a očima jejich, kteréž smilníce, chodily za ukydanými bohy svými, a tak sami se býti hodné ošklivosti seznají pro nešlechetnosti, kteréž páchali ve všech ohavnostech svých.
Sa’an nan a cikin al’ummai inda aka kai ku zaman bauta, waɗanda suka a tsere za su tuna da ni, yadda raina ya ɓaci ta wurin zukatansu marasa imani, waɗanda suka rabu da ni, da kuma ta wurin idanunsu, waɗanda suka yi sha’awace-sha’awacen gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu saboda mugayen abubuwan da suka aikata.
10 A zvědí, že já jsem Hospodin, a že jsem ne nadarmo mluvil, že na ně uvedu zlé toto.
Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji; ba a banza na ce zan kawo musu wannan masifa ba.
11 Takto praví Panovník Hospodin: Tleskni rukou svou, a dupni nohou svou, a rci: Nastojte na dům Izraelský, že pro všecky ohavnosti nejhorší mečem, hladem a morem padnouti mají.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ku tafa hannuwanku tare ku kuma taka ƙafafunku ku yi ihu ku ce, “Kaito!” Saboda dukan mugaye da kuma abubuwan banƙyama na gidan Isra’ila, gama za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba.
12 Ten, kdož daleko bude, morem umře, a kdo blízko, mečem padne, ostatní pak a obležený hladem umře, a tak docela vyleji prchlivost svou na ně.
Wanda yake da nisa zai mutu da annoba, shi da yake kusa kuma zai mutu ta takobi, wanda kuma ya tsira aka kuma bari zai mutu da yunwa. Ta haka zan aukar da fushina a kansu.
13 A zvíte, že já jsem Hospodin, když budou zbití jejich u prostřed ukydaných bohů jejich vůkol oltářů jejich, na všelikém pahrbku vysokém, na všech vrších hor, a pod všelikým dřevem zeleným, i pod všelikým dubem hustým, na kterémkoli místě obětovávali vůni libou všelikým ukydaným bohům svým.
Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da gawawwakin mutanensu suna kwance a kusa da gumakansu da kewaye da bagadansu, a kowane kan tudu mai tsawo da kuma a kan dukan kan duwatsu, a ƙarƙashin kowane inuwar itace da kuma kowane oak mai ganye, wuraren da suke ƙone turare masu ƙanshi wa dukan gumakansu.
14 Nebo vztáhnu ruku svou na ně, a učiním zemi tuto zpustlou, zpustlejší než poušť Diblat, po všech obydlích jejich. I zvědí, že já jsem Hospodin.
Zan kuma miƙa hannuna a kansu in mai da ƙasarsu kango daga hamadan Dibila, a duk inda suke zama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”