< 2 Mojžišova 9 >

1 Tedy řekl Hospodin Mojžíšovi: Vejdi k Faraonovi, a mluv k němu: Takto praví Hospodin, Bůh Hebrejský: Propusť lid můj, ať mi slouží.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
2 Pakli nebudeš chtíti propustiti, než předce držeti je budeš:
In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
3 Aj, ruka Hospodinova bude na dobytku tvém, kterýž jest na poli, na koních, na oslích, na velbloudích, na volích a na ovcech, mor těžký velmi.
hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
4 A učiní Hospodin rozdíl mezi dobytky Izraelských a mezi dobytky Egyptských, aby nic neumřelo ze všeho, což jest synů Izraelských.
Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
5 A uložil Hospodin čas jistý, řka: Zítra učiní Hospodin věc takovou na zemi.
Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
6 I učinil Hospodin tu věc na zejtří, a pomřel všecken dobytek Egyptským; z dobytku pak synů Izraelských ani jedno neumřelo.
Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
7 I poslal Farao, a aj, neumřelo z dobytků Izraelských ani jedno. Ale obtíženo jest srdce Faraonovo, a nepropustil lidu.
Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
8 I řekl Hospodin Mojžíšovi a Aronovi: Vezměte sobě plné hrsti své popela z peci, a ať jej sype Mojžíš k nebi před očima Faraonovýma.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
9 I obrátí se v prach po vší zemi Egyptské, a budou z něho na lidech i na hovadech vředové prýštící se neštovicemi po vší zemi Egyptské.
Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
10 Nabravše tedy popela z peci, stáli před Faraonem, a sypal jej Mojžíš k nebi. I byli vředové plní neštovic, prýštící se na lidech i na hovadech.
Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
11 Aniž mohli čarodějníci státi před Mojžíšem pro vředy; nebo byli vředové na čarodějnících i na všech Egyptských.
Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
12 I zsilil Hospodin srdce Faraonovo, a neposlechl jich, tak jakž byl mluvil Hospodin k Mojžíšovi.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
13 Tedy řekl Hospodin Mojžíšovi: Vstana ráno, postav se před Faraonem, a rci k němu: Takto praví Hospodin, Bůh Hebrejský: Propusť lid můj, ať mi slouží.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
14 Nebo já teď již pošli všecky rány své na srdce tvé, i na služebníky tvé a na lid tvůj, abys věděl, žeť není podobného mně na vší zemi.
ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
15 Nebo nyní, když jsem vztáhl ruku svou, byl bych tebe také ranil i lid tvůj morem tím; a tak bys byl vyhlazen z země.
Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
16 Ale však proto jsem tě zachoval, abych ukázal na tobě moc svou, a aby vypravovali jméno mé na vší zemi.
Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
17 Ještě ty pozdvihuješ se proti lidu mému, nechtěje ho propustiti?
Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
18 Aj, já dštíti budu zítra v tentýž čas krupobitím těžkým náramně, jakéhož nebylo v Egyptě od toho dne, jakž založen jest, až do tohoto času.
Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
19 Protož nyní pošli, shromažď dobytek svůj a cokoli máš na poli. Na všecky lidi i hovada, kteráž by nalezena byla na poli, a nebyla by shromážděna do domu, spadne krupobití, a pomrou.
Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
20 Kdo tedy z služebníků Faraonových ulekl se slova Hospodinova, svolal hbitě služebníky své i dobytek svůj do domu.
Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
21 Ale kdož nepřiložil srdce svého k slovu Hospodinovu, nechal služebníků svých a dobytka svého na poli.
Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
22 I řekl Hospodin Mojžíšovi: Vztáhni ruku svou k nebi, ať jest krupobití po vší zemi Egyptské, na lidi i na hovada i na všelikou bylinu polní v zemi Egyptské.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
23 Tedy vztáhl Mojžíš hůl svou k nebi, a Hospodin vydal hřímání a krupobití. I sstoupil oheň na zem, a dštil Hospodin krupobitím na zemi Egyptskou.
Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
24 I bylo krupobití a oheň smíšený s krupobitím těžký velmi, jakéhož nebylo nikdy ve vší zemi Egyptské, jakž v ní bydliti lidé začali.
ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
25 I ztloukly kroupy po vší zemi Egyptské, cožkoli bylo na poli od člověka až do hovada; všecku také bylinu polní potloukly kroupy, i všecko stromoví na poli zpřerážely.
Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
26 Toliko v zemi Gesen, v níž byli synové Izraelští, nebylo krupobití.
Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
27 Poslav tedy Farao, povolal Mojžíše a Arona a řekl jim: Zhřešil jsem i nyní. Hospodinť jest spravedlivý, ale já a lid můj bezbožní jsme.
Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
28 Modlte se Hospodinu, (nebo dosti jest), ať není hřímání Božího a krupobití. Tedy propustím vás, aniž déle zůstávati budete.
Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
29 I řekl jemu Mojžíš: Když vyjdu ven z města, rozprostru ruce své k Hospodinu, a hřímání přestane, i krupobití více nebude, abys poznal, že Hospodinova jest země.
Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
30 Ale vím, že ani ty, ani služebníci tvoji ještě se nebudete báti tváři Hospodina Boha.
Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
31 I potlučen jest len a ječmen; nebo ječmen se byl vymetal, len také byl v hlávkách.
(Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
32 Ale pšenice a špalda nebyla ztlučena, nebo pozdní byla.
Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
33 Tedy Mojžíš vyšed od Faraona z města, rozprostřel ruce své k Hospodinu. I přestalo hřímání a krupobití, a ani déšť nelil se na zemi.
Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
34 Uzřev pak Farao, že přestal déšť a krupobití a hřímání, opět hřešil; a více obtížil srdce své, on i služebníci jeho.
Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
35 I zsililo se srdce Faraonovo, a nepropustil synů Izraelských, tak jakž byl mluvil Hospodin skrze Mojžíše.
Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.

< 2 Mojžišova 9 >