< Skutky Apoštolů 1 >
1 První zajisté knihu sepsalť jsem, ó Teofile, o všech věcech, kteréž začal Ježíš činiti a učiti,
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 Až do toho dne, v kterémžto dav přikázání apoštolům, kteréž byl skrze Ducha svatého vyvolil, vzhůru vzat jest.
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 Kterýmžto i zjevoval sebe samého živého po svém umučení ve mnohých jistých důvodích, za čtyřidceti dnů ukazuje se jim a mluvě o království Božím.
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 A shromáždiv se s nimi, přikázal jim, aby z Jeruzaléma neodcházeli, ale aby očekávali zaslíbení Otcova, o kterémž jste prý slyšeli ode mne.
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 Nebo Jan zajisté křtil vodou, ale vy pokřtěni budete Duchem svatým po nemnohých těchto dnech.
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 Oni pak sšedše se, otázali se ho, řkouce: Pane, v tomto-li času napravíš království Izraelské?
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 I řekl jim: Neníť vaše věc znáti časy anebo příhodnosti časů, kteréžto Otec v moci své položil.
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8 Ale přijmete moc Ducha svatého, přicházejícího na vás, a budete mi svědkové, i v Jeruzalémě, i ve všem Judstvu, i v Samaří, a až do posledních končin země.
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 A to pověděv, ani na to hledí, vzhůru vyzdvižen jest, a oblak vzal jej od očí jejich.
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 A když za ním v nebe jdoucím pilně hleděli, aj, dva muži postavili se podle nich v rouše bílém,
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 A řekli: Muži Galilejští, co stojíte, hledíce do nebe? Tento Ježíš, kterýž vzhůru vzat jest od vás do nebe, takť přijde, jakž jste spatřili způsob jeho jdoucího do nebe.
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Tedy navrátili se do Jeruzaléma od hory, jenž slove Olivetská, kteráž jest blízko Jeruzaléma, vzdálí cesty jednoho dne svátečního.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 A když přišli domů, vstoupili do vrchního příbytku domu, kdež přebývali, i Petr i Jakub, i Jan a Ondřej, Filip a Tomáš, Bartoloměj a Matouš, Jakub Alfeův a Šimon Zelótes a Judas bratr Jakubův.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 Ti všickni byli trvajíce jednomyslně na modlitbě a pokorné prosbě s ženami a s Marijí, matkou Ježíšovou, i s bratřími jeho.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 V těch pak dnech povstav Petr uprostřed učedlníků, řekl (a byl zástup lidí spolu shromážděných okolo sta a dvadcíti):
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 Muži bratří, musilo se naplniti Písmo to, kteréž předpověděl Duch svatý skrze ústa Davidova o Jidášovi, kterýž byl vůdce těch, jenž jímali Ježíše.
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 Nebo byl přičten k nám, a byl došel losu přisluhování tohoto.
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 Ten zajisté obdržel pole ze mzdy nepravosti, a oběsiv se, rozpukl se na dvé, i vykydla se všecka střeva jeho.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 A to známé jest učiněno všechněm přebývajícím v Jeruzalémě, takže jest nazváno pole to vlastním jazykem jejich Akeldama, to jest pole krve.
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 Psáno jest zajisté v knihách Žalmů: Budiž příbytek jeho pustý, a nebuď, kdo by přebýval v něm, a opět: Biskupství jeho vezmi jiný.
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 Protož musíť to býti, aby jeden z těch mužů, kteříž jsou s námi bývali po všecken čas, v němž přebýval mezi námi Pán Ježíš,
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 Počav od křtu Janova až do dne toho, v kterémžto vzhůru vzat jest od nás, byl svědkem spolu s námi vzkříšení jeho.
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 Tedy postavili dva, Jozefa, jenž sloul Barsabáš, kterýž měl příjmí Justus, a Matěje.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 A modléce se, řekli: Ty, Pane, všech srdcí zpytateli, ukažiž, kterého jsi vyvolil z těchto dvou,
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
25 Aby přijal los přisluhování tohoto a apoštolství, z něhož jest vypadl Jidáš, aby odšel na místo své.
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 I dali jim losy. Spadl pak los na Matěje, i připojen jest z společného snešení k jedenácti apoštolům.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.