< Skutky Apoštolů 4 >

1 A když oni mluvili k lidu, přišli kněží a úředník chrámu a saduceové,
Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
2 Těžce to nesouce, že lid učili a zvěstovali ve jménu Ježíše vzkříšení z mrtvých.
Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
3 I vztáhli na ně ruce a vsadili je do žaláře až do jitra, neb již byl večer.
Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
4 Mnozí pak z těch, kteříž slyšeli slovo Boží, uvěřili. I učiněn jest počet mužů okolo pěti tisíců.
Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
5 Stalo se pak nazejtří, sešli se knížata jejich, a starší, a zákoníci v Jeruzalémě,
Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
6 A Annáš nejvyšší kněz, a Kaifáš, a Jan, a Alexander, a kteřížkoli byli z pokolení nejvyššího kněze.
Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
7 I postavivše je mezi sebou, otázali se jich: Jakou mocí aneb v kterém jménu učinili jste to vy?
Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
8 Tedy Petr, jsa pln Ducha svatého, řekl jim: Knížata lidu a starší Izraelští,
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
9 Poněvadž my dnes k soudu jsme přivedeni pro dobrodiní člověku nemocnému učiněné, kterak by on zdráv učiněn byl:
In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
10 Známo buď všechněm vám i všemu lidu Izraelskému, že ve jménu Ježíše Krista Nazaretského, kteréhož jste vy ukřižovali, jehož Bůh vzkřísil z mrtvých, skrze toho jméno tento stojí před vámi zdravý.
to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
11 Toť jest ten kámen za nic položený od vás dělníků, kterýž učiněn jest v hlavu úhelní.
Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
12 A neníť v žádném jiném spasení; neboť není jiného jména pod nebem daného lidem, skrze kteréž bychom mohli spaseni býti.
Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
13 I vidouce takovou udatnost a smělost v mluvení Petrovu a Janovu, a shledavše, že jsou lidé neučení a prostí, divili se, a poznali je, že s Ježíšem bývali.
Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
14 Èlověka také toho vidouce, an stojí s nimi, kterýž byl uzdraven, neměli co mluviti proti nim.
Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
15 I rozkázavše jim vystoupiti z rady, rozmlouvali vespolek,
Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
16 Řkouce: Co učiníme lidem těmto? Nebo že jest zjevný zázrak stal se skrze ně, všem přebývajícím v Jeruzalémě známé jest, aniž můžeme toho zapříti.
Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
17 Ale aby se to více nerozhlašovalo v lidu, s pohrůžkou přikažme jim, aby více v tom jménu žádnému z lidí nemluvili.
Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
18 I povolavše jich, přikázali jim, aby nikoli nemluvili, ani učili ve jménu Ježíšovu.
Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
19 Tedy Petr a Jan odpovídajíce, řekli jim: Jest-li to spravedlivé před obličejem Božím, abychom vás více poslouchali než Boha, suďte.
Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
20 Nebť nemůžeme nemluviti toho, co jsme viděli a slyšeli.
Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
21 A oni pohrozivše jim, propustili je, nenalezše na nich příčiny trestání, pro lid; nebo všickni velebili Boha z toho, co se bylo stalo.
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 Byl zajisté v letech více než ve čtyřidcíti člověk ten, při kterémž se byl stal zázrak ten uzdravení.
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
23 A jsouce propuštěni, přišli k svým a pověděli jim, co k nim přední kněží a starší mluvili.
Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
24 Kteříž uslyševše to, jednomyslně pozdvihli hlasu k Bohu a řekli: Hospodine, ty jsi Bůh, kterýž jsi učinil nebe i zemi, i moře i všecko, což v nich jest,
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
25 Kterýž jsi skrze ústa Davida, služebníka svého, řekl: Proč jsou se bouřili národové a lidé myslili marné věci?
Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
26 Postavili se králové zemští, a knížata sešla se vespolek proti Pánu a proti Pomazanému jeho.
Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
27 Právěť jsou se jistě sešli proti svatému Synu tvému Ježíšovi, kteréhož jsi pomazal, Herodes a Pontský Pilát, s pohany a lidem Izraelským,
Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
28 Aby učinili to, což ruka tvá a rada tvá předuložila, aby se stalo.
Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
29 A nyní, Pane, pohlediž na pohrůžky jejich a dejž služebníkům svým mluviti slovo tvé svobodně a směle,
Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
30 Vztahuje ruku svou k uzdravování a k činění divů a zázraků, skrze jméno svatého Syna tvého Ježíše.
Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 A když se oni modlili, zatřáslo se to místo, na kterémž byli shromážděni, a naplněni jsou všickni Duchem svatým, a mluvili slovo Boží směle a svobodně.
Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
32 Toho pak množství věřících bylo jedno srdce a jedna duše. Aniž kdo co z těch věcí, kteréž měl, svým vlastním býti pravil, ale měli všecky věci obecné.
Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
33 A mocí velikou vydávali apoštolé svědectví o vzkříšení Pána Ježíše, a milost veliká přítomná byla všechněm jim.
Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
34 A žádný mezi nimi nebyl nuzný; nebo kteřížkoli měli pole nebo domy, prodávajíce, přinášeli peníze, za kteréž prodávali,
Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
35 A kladli před nohy apoštolské. I rozdělováno bylo jednomu každému, jakž komu potřebí bylo.
su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
36 Jozes pak, kterýž příjmí měl od apoštolů Barnabáš, (což se vykládá syn utěšení, ) z pokolení Levítského, z Cypru rodem,
Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
37 Měv pole, prodal je, a přinesl peníze, a položil k nohám apoštolským.
ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.

< Skutky Apoštolů 4 >