< 2 Timoteovi 2 >

1 Protož ty, synu můj, zmocniž se v milosti, kteráž jest v Kristu Ježíši.
Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
2 A což jsi slyšel ode mne před mnohými svědky, svěřujž to lidem věrným, kteříž by způsobní byli i jiné učiti.
Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
3 A tak ty snášej protivenství, jako ctný rytíř Ježíše Krista.
Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
4 Žádný, kdož rytěřuje, neplete se v obecné živnosti, aby se svému hejtmanu líbil.
Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
5 A jestliže by kdo i bojoval, nebudeť korunován, leč by řádně bojoval.
Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
6 Pracovati musí i oráč, prve nežli užitku okusí.
Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
7 Rozuměj, coť pravím, a dejž tobě Pán ve všem smysl pravý.
Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
8 Pamatujž na to, že Ježíš Kristus vstal z mrtvých, jenž jest z semene Davidova, podle evangelium mého.
Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
9 V kterémžto protivenství trpím, až i vězení, jako bych zločinec byl, ale slovo Boží není u vězení.
wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
10 Protož všecko to snáším pro vyvolené Boží, aby i oni spasení došli, kteréžto jest v Kristu Ježíši, s slavou věčnou. (aiōnios g166)
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios g166)
11 Věrná jest tato řeč. Nebo jestližeť jsme s ním zemřeli, tedy také spolu s ním živi budeme.
Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
12 A trpíme-liť, budeme také spolu s ním kralovati; pakli ho zapíráme, i onť nás zapře.
in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
13 A jsme-liť nevěrní, onť zůstává věrný; zapříti sám sebe nemůže.
in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
14 Tyto věci připomínej, s osvědčováním před obličejem Páně, a ať se o slova nevadí, nebo to k ničemu není užitečné, ale jest ku podvrácení posluchačů.
Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
15 Pilně se snažuj vydati sebe Bohu milého dělníka, za nějž by se nebylo proč styděti, a kterýž by právě slovo pravdy rozděloval.
Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
16 Bezbožných pak těch křiků daremních varuj se, neboť velmi rozmnožují bezbožnost,
Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
17 A řeč jejich jako rak rozjídá se. Z nichžto jest Hymeneus a Filétus,
Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
18 Kteříž při pravdě pobloudili od cíle, pravíce, že by se již stalo vzkříšení, a převracejí víru některých.
waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
19 Ale pevný základ Boží stojí, maje znamení toto: Znáť Pán ty, kteříž jsou jeho, a opět: Odstup od nepravosti každý, kdož vzývá jméno Kristovo.
Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
20 V domu pak velikém netoliko jsou nádoby zlaté a stříbrné, ale také dřevěné i hliněné, a některé zajisté ke cti, některé pak ku potupě.
A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
21 Protož jestliže by se kdo očistil od těch věcí, bude nádobou ke cti, posvěcenou, a užitečnou Pánu, ke všelikému skutku dobrému hotovou.
In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
22 Mládenčích pak žádostí utíkej, ale následuj spravedlnosti, víry, lásky, pokoje, s těmi, kteříž vzývají Pána z srdce čistého.
Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 Bláznivých pak a nevzdělavatelných otázek varuj se, věda, že plodí sváry.
Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
24 Na služebníka pak Božího nesluší vaditi se, ale aby byl přívětivý ke všem, způsobný k učení, trpělivý,
Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
25 Kterýž by v tichosti vyučoval ty, jenž se pravdě protiví, zda by někdy dal jim Bůh pokání ku poznání pravdy,
Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
26 Aby sami k sobě přijdouce, dobyli se z osidla ďáblova, od něhož jsou zjímáni k vykonávání jeho vůle.
su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.

< 2 Timoteovi 2 >