< 2 Královská 25 >

1 Stalo se pak léta devátého kralování jeho, měsíce desátého, v desátý den téhož měsíce, že přitáhl Nabuchodonozor král Babylonský se vším vojskem svým k Jeruzalému, a položil se u něho, a vzdělali proti němu hradbu vůkol.
A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
2 A bylo město obleženo, až do jedenáctého léta krále Sedechiáše.
Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
3 V kterémžto, devátého dne čtvrtého měsíce, rozmohl se hlad v městě, a neměl chleba lid země.
A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
4 I protrženo jest město, a všickni muži bojovní utekli noci té skrze bránu mezi dvěma zdmi u zahrady královské; Kaldejští pak leželi okolo města. Ušel také král cestou pouště.
Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
5 I honilo vojsko Kaldejské krále, a postihli ho na rovinách Jerišských, a všecko vojsko jeho rozprchlo se od něho.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
6 A tak javše krále, přivedli jej k králi Babylonskému do Ribla, kdež učinili o něm soud.
Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
7 Syny pak Sedechiášovy zmordovali před očima jeho. Potom Sedechiáše oslepili, a svázavše ho řetězy ocelivými, zavedli jej do Babylona.
Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
8 Potom měsíce pátého, sedmý den téhož měsíce, léta devatenáctého kralování Nabuchodonozora krále Babylonského, přitáhl Nebuzardan hejtman nad žoldnéři, služebník krále Babylonského, do Jeruzaléma.
A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
9 A zapálil dům Hospodinův i dům královský, i všecky domy v Jeruzalémě, a tak všecky domy veliké vypálil.
Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
10 Zdi také Jeruzalémské vůkol pobořilo všecko vojsko Kaldejské, kteréž bylo s tím hejtmanem nad žoldnéři.
Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
11 Ostatek pak lidu, kterýž byl zůstal v městě, i poběhlce, kteříž se byli obrátili k králi Babylonskému, a jiný obecný lid, zavedl Nebuzardan hejtman nad žoldnéři.
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
12 Toliko něco chaterného lidu země zanechal hejtman nad žoldnéři, aby byli vinaři a oráči.
Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
13 Nadto sloupy měděné, kteříž byli v domě Hospodinově, i podstavky, i moře měděné, kteréž bylo v domě Hospodinově, ztloukli Kaldejští, a měď z nich odvezli do Babylona.
Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
14 Též hrnce, lopaty a nástroje hudebné, a kadidlnice i všecky nádoby měděné, jimiž sloužili, pobrali.
Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
15 I nádoby k oharkům a kotlíky, a cokoli zlatého a stříbrného bylo, pobral hejtman nad žoldnéři,
Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
16 Sloupy dva, moře jedno a podstavky, jichž byl nadělal Šalomoun do domu Hospodinova. Nebylo váhy mědi všech těch nádob.
Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
17 Osmnácti loket byla výška sloupu jednoho, a makovice na něm měděná, kterážto makovice tří loket zvýší byla, a mřežování i jablka zrnatá na té makovici vůkol; všecko bylo měděné. Takovýž byl i druhý sloup s mřežováním.
Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
18 Vzal také týž hejtman nad žoldnéři Saraiáše kněze předního, a Sofoniáše kněze nižšího, a tři strážné prahu.
Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
19 A z města vzal komorníka jednoho, kterýž byl hejtmanem nad muži bojovnými, a pět mužů z těch, jenž bývali při králi, kteříž nalezeni byli v městě, a předního spisovatele vojska, kterýž popisoval vojsko z lidu země, a šedesáte mužů z lidu země, kteříž se nalezli v městě.
Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
20 Zjímav tedy je Nebuzardan hejtman nad žoldnéři, přivedl je k králi Babylonskému do Ribla.
Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
21 I pobil je král Babylonský, a zmordoval je v Ribla, v zemi Emat, a tak zaveden jest Juda z země své.
A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
22 Lidu pak, kterýž zůstal v zemi Judské, jehož byl zanechal Nabuchodonozor král Babylonský, představil Godoliáše syna Achikama, syna Safanova.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
23 I uslyšeli všickni hejtmané vojska, oni i lid jejich, že postavil za správce král Babylonský Godoliáše, a přišli k Godoliášovi do Masfa, totiž Izmael syn Netaniášův, a Jochanan syn Kareachův, a Saraiáš syn Tanchumeta Netofatského, a Jazaniáš syn Machatův, oni i lid jejich.
Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
24 Tedy přisáhl jim Godoliáš i lidu jejich, a řekl jim: Nebojte se služby Kaldejských, zůstaňte v zemi, a služte králi Babylonskému, a dobře vám bude.
Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
25 I stalo se měsíce sedmého, přišel Izmael syn Netaniáše, syna Elisamova, z semene královského, a deset mužů s ním. I zabili Godoliáše, a umřel; takž i Židy i Kaldejské, kteříž s ním byli v Masfa.
Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
26 Pročež zdvih se všecken lid, od malého až do velikého, i hejtmané vojsk, ušli do Egypta; nebo se báli Kaldejských.
Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
27 Stalo se také léta třidcátého sedmého po zajetí Joachina krále Judského, dvanáctého měsíce, dvadcátého sedmého dne téhož měsíce, povýšil Evilmerodach král Babylonský toho léta, když počal kralovati, Joachina krále Judského, pustiv ho z žaláře.
A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
28 A mluvil s ním dobrotivě, i stolici jeho postavil nad stolice jiných králů, kteříž s ním byli v Babyloně.
Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
29 Změnil též roucho jeho, kteréž měl v žaláři. I jídal vždycky před ním po všecky dny života svého.
Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
30 Nebo vyměřený pokrm ustavičně dáván byl jemu od krále, a to na každý den po všecky dny života jeho.
Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.

< 2 Královská 25 >